AYU 25

Bildad Bai Yarda Allah Zai Baratar da Mutum Ba

1 Bildad ya amsa.

2 “Allah mai iko ne, duka sai a ji tsoronsa,

A samaniya yake tafiya da mulkinsa da salama.

3 Akwai wanda zai iya ƙidaya mala’ikun da suke masa hidima?

Akwai wurin da hasken Allah bai haskaka ba?

4 Akwai wanda ya isa ya zama adali,

Ko mai tsarki a gaban Allah?

5 Hasken wata ba haske ba ne a gare shi,

Ko taurari ma ba su da tsarki a gabansa.

6 To, mutum fa? Ai, wannan tsutsa ne, ɗan ƙwaro kawai.

Me mutum ya daɗa a gaban Allah?”