FAR 49

Faɗar Yakubu a kan ‘Ya’yansa

1 Yakubu ya kirawo ‘ya’yansa maza, ya ce, “Ku tattaru wuri ɗaya don in faɗa muku abin da zai same ku a cikin kwanaki masu zuwa.

2 “Ku taru ku ji, ya ku ‘ya’yan

Yakubu, maza,

Ku kuma kasa kunne ga Isra’ila

mahaifinku.

3 “Ra’ubainu, kai ɗan farina

ne, ƙarfina,

Ɗan balagata, isasshe kuma, mafi

ƙarfi duka cikin ‘ya’yana.

4 Kamar ambaliyar ruwa mai fushi

kake,

Amma ba za ka zama mafi daraja

ba,

Domin ka hau gadon mahaifinka,

Sa’an nan ka ƙazantar da shi.

5 “Saminu da Lawi ‘yan’uwa ne,

Suka mori takubansu cikin ta da

hankali.

6 Ba zan shiga shawararsu ta asiri ba,

Ba kuwa zan sa hannu cikin taronsu

ba,

Gama cikin fushinsu suka kashe

mutane,

Cikin gangancinsu kuma suka

gurgunta bijimai.

7 La’ananne ne fushinsu domin mai

tsanani ne,

Da hasalarsu kuma, gama bala’i ce.

Zan warwatsa su cikin dukan ƙasar

Yakubu,

In ɗaiɗaitar su su cikin Isra’ilawa.

8 “Yahuza, ‘yan’uwanka za su yabe

ka,

Za ka shaƙe wuyan maƙiyanka,

‘Yan’uwanka za su rusuna a

gabanka.

9 Yahuza ɗan zaki ne,

Ya kashe ganima sa’an nan ya komo

wurin ɓuyarsa.

Yahuza kamar zaki yake,

Yakan kwanta a miƙe,

Ba mai ƙarfin halin da zai tsokane

shi.

10 Yana riƙe da sandan mulkinsa,

Ya sa shi a tsakanin ƙafafunsa,

Har Shilo ya zo.

Zai mallaki dukan jama’o’i.

11 Zai ɗaure aholakinsa a kurangar

inabi,

A kuranga mafi kyau,

Zai wanke tufafinsa da ruwan inabi,

Ruwan inabi ja wur kamar jini.

12 Idanunsa za su yi ja wur saboda shan

ruwan inabi,

Haƙoransa kuma su yi fari fat

saboda shan madara.

13 “Zabaluna zai zauna a gefen teku,

Zai zama tashar jiragen ruwa,

Kan iyakarsa kuma zai kai har

Sidon.

14 “Issaka alfadari ne ƙaƙƙarfa,

Ya kwanta a miƙe tsakanin

jakunkunan shimfiɗa.

15 Saboda ya ga wurin hutawa ne mai

kyau,

Ƙasar kuma mai kyau ce,

Sai ya sunkuyar da kafaɗunsa domin

ɗaukar kaya,

Ya zama bawa, yana yin aiki mai

wuya.

16 “Dan zai zama mai mulki ga

mutanensa

Kamar ɗaya daga cikin kabilan

Isra’ila.

17 Dan zai zama maciji a gefen hanya,

Zai zama kububuwa a gefen turba,

Mai saran diddigen doki

Don mahayin ya fāɗi da baya.

18 Ina zuba ido ga cetonka, ya

Ubangiji.

19 “Gad, ‘yan fashi za su kai masa hari,

Shi kuwa zai runtume su.

20 “Ashiru, ƙasarsa za ta ba da amfani

mai yawa,

Zai kuma yi tanadin abincin da ya

dace da sarki.

21 “Naftali sakakkiyar barewa ce,

Mai haihuwar kyawawan ‘ya’ya.

22 “Yusufu jakin jeji ne,

Jakin jeji a gefen maɓuɓɓuga

Aholakan jeji a gefen tuddai.

23 Maharba suka tasar masa ba tausayi

Suka fafare shi da kwari da baka.

24 Duk da haka bakunansu sun

kakkarye.

Damatsansu sun yayyage

Ta wurin ikon Allah Mai Girma na

Yakubu,

Makiyayi, Dutse na Isra’ila.

25 Ta wurin Allah na mahaifinka wanda

zai taimake ka,

Ta wurin Allah Mai Iko Dukka

wanda zai sa maka albarka

Albarkun ruwan sama daga bisa,

Da na zurfafa daga ƙarƙashin

ƙasa,

Da albarkun mama da na mahaifa.

26 Albarkun hatsi da na gari

Albarkun daɗaɗɗun duwatsu,

Abubuwan jin daɗi na madawwaman

tuddai,

Allah ya sa su zauna a kan Yusufu,

Da a goshin wanda aka raba shi da

‘yan’uwansa.

27 “Biliyaminu kyarkeci ne mai kisa,

Da safe yakan cinye abin da ya

kaso,

Da maraice kuma yakan raba abin da

ya kamo.”

28 Waɗannan duka su ne kabilan Isra’ila goma sha biyu, wannan kuma shi ne abin da mahaifinsu ya faɗa musu sa’ad da yake sa musu albarka. Ya sa wa kowannensu albarka da irin albarkar da ta cancance shi.

Rasuwar Yakubu da Jana’izarsa

29 Yakubu ya umarce su, ya ce musu, “Ga shi, lokacin mutuwa ya gabato da za a kai ni wurin jama’ata da suka riga ni. Sai ku binne ni tare da kakannina a cikin kogon da yake a saurar Efron Bahitte,

30 a cikin kogon da yake a Makfela, gabashin Mamre, a ƙasar Kan’ana, wanda Ibrahim ya saya duk da saurar, daga wurin Efron Bahitte, ya zama mallakarsa don makabarta.

31 A can aka binne Ibrahim da Saratu matarsa. A can kuma suka binne Ishaku da Rifkatu matarsa. A can kuma na binne Lai’atu.

32 Da saurar da kogon da yake cikinta, an saye su daga Hittiyawa.”

33 Sa’ad da Yakubu ya gama yi wa ‘ya’yansa maza wasiyya, sai ya hau da ƙafafunsa bisa kan gado, Ya ja numfashinsa na ƙarshe, aka kuwa kai shi ga jama’arsa waɗanda suka riga shi.