NEH 7

Nehemiya Ya Zaɓi Masarautan Urushalima

1 Sa’ad da aka gina garun, aka sa ƙofofinsa, aka kuma sa matsaran ƙofofi, da mawaƙa, da Lawiyawa,

2 sai na ba ɗan’uwana, Hanani, da Hananiya, shugaban kagara, aikin riƙon Urushalima. Shi Hananiya mai aminci ne, mai tsoron Allah, fiye da sauran mutane.

3 Sa’an nan na ce musu, kada su buɗe ƙofofin Urushalima da sassafe, sai rana ta cira sosai, su kuma kulle ƙofofin da ƙarfe kafin matsara su tashi wajen faɗuwar rana. Su samo matsara daga mazaunan Urushalima, su sa su tsaye a muhimman wurare, waɗansunsu kuma suna zaga gidaje.

Lissafin Mutane

4 Birnin yana da faɗi da girma, amma mutanen da suke ciki kaɗan ne, ba a kuma gina gidaje ba tukuna.

5 Allahna kuwa ya sa a zuciyata in tara manya da shugabanni, da sauran jama’a don a rubuta su bisa ga asalinsu. Na sami littafin asali na waɗanda suka fara komowa. Ga abin da na tarar aka rubuta ciki.

6 Waɗannan su ne mutanen lardin Yahuza, waɗanda suka komo daga zaman talala da Nebukadnezzar Sarkin Babila ya kai mutane. Sun komo Urushalima da Yahuza. Kowa ya tafi garinsu.

7 Sun komo tare da Zarubabel, da Yeshuwa, da Nehemiya, da Seraiya, da Re’elaya, da Nahamani, da Mordekai, da Bilshan, da Misfar, da Bigwai, da Rehum, da Ba’ana.

8-25 Ga jerin iyalan Isra’ila da adadin waɗanda suka komo daga zaman dole

iyalin Farosh, dubu biyu da ɗari da saba’in da biyu (2,172)

iyalin Shefatiya, ɗari uku da saba’in da biyu

iyalin Ara, ɗari shida da hamsin da biyu

iyalin Fahat-mowab, wato zuriyar Yeshuwa da Yowab, dubu biyu da ɗari takwas da goma sha takwas (2,818)

iyalin Elam, dubu da ɗari biyu da hamsin da huɗu (1,254)

iyalin Zattu, ɗari takwas da arba’in da biyar

iyalin Zakkai, ɗari bakwai da sittin

iyalin Bani, ɗari shida da arba’in da takwas

iyalin Bebai, ɗari shida da ashirin da takwas

iyalin Azgad, dubu biyu da ɗari uku da ashirin da biyu (2,322)

iyalin Adonikam, ɗari shida da sittin da bakwai

iyalin Bigwai, dubu biyu da sittin da bakwai (2,067)

iyalin Adin, ɗari shida da hamsin da biyar

iyalin Ater (na Hezekiya), tasa’in da takwas

iyalin Hashum, ɗari uku da ashirin da takwas

iyalin Bezai, ɗari uku da ashirin da huɗu

iyalin Yora, ɗari da goma sha biyu

iyalin Gibeyon, tasa’in da biyar

26-38 Mutanen da kakanninsu suka zauna a waɗannan garuruwa, su ma sun komo daga zaman talala.

Baitalami da Netofa, ɗari da tamanin da takwas

Anatot, ɗari da ashirin da takwas

Azmawet, arba’in da biyu

Kiriyat-yeyarim da Kefira, da Biyerot, ɗari bakwai da arba’in da uku

Rama da Geba, ɗari shida da ashirin da ɗaya

Mikmash, ɗari da ashirin da biyu

Betel da Ai, ɗari da ashirin da uku

Da wani Nebo, hamsin da biyu

Da wani Elam, dubu da ɗari biyu da hamsin da huɗu (1,254)

Harim, ɗari uku da ashirin

Yariko, ɗari uku da arba’in da biyar

Lod, da Hadid, da Ono, ɗari bakwai da ashirin da ɗaya

Senaya, dubu uku da ɗari tara da talatin (3,930)

39-42 Ga lissafin iyalin firistoci da suka komo daga zaman talala.

Yedaiya, na zuriyar Yeshuwa, ɗari tara da saba’in da uku

Immer, dubu ɗaya da hamsin da biyu (1,052)

Fashur, dubu da ɗari biyu da arba’in da bakwai (1,247)

Harim, dubu ɗaya da goma sha bakwai (1,017)

43 Lawiyawan da suka komo daga zaman talala, Yeshuwa da Kadmiyel na zuriyar Hodawiya, saba’in da huɗu.

44 Mawaƙa, na zuriyar Asaf, ɗari da arba’in da takwas.

45 Masu tsaron Haikali su ne zuriyar Shallum, da Ater, da Talmon, da Akkub, da Hatita, da Shobai, ɗari da talatin da takwas.

46-56 Ma’aikatan Haikali da suka komo daga zaman talala, su ne

Zuriyar Ziha, da Hasufa, da Tabbawot,

Keros, da Siyaha, da Fadon,

Lebana, da Hagaba, da Shamlai,

Hanan, da Giddel, da Gahar,

Rewaiya, da Rezin, da Nekoda,

Gazam, da Uzza, da Faseya,

Besai, da Me’uniyawa, da Nefushiyawa,

Bakbuk, da Hakufa, da Harkur,

Bazlut, da Mehida, da Harsha,

Barkos, da Sisera, da Tema,

Neziya, da Hatifa.

57-59 Iyalan barorin Sulemanu da suka komo daga zaman talala, su ne

na Sotai, da Hassoferet, da Feruda,

Yawala, da Darkon, da Giddel,

Shefatiya, da Hattil, da Fokeret-hazzebayim, da Ami.

60 Jimillar zuriyar ma’aikatan Haikali da na Sulemanu, su ɗari uku da tasa’in da biyu ne.

61-62 Waɗannan su ne daga zuriyar Delaiya, da Tobiya, da Nekoda, waɗanda suka zo daga garuruwan Telmela, da Tel-harsha, da Kerub, da Addan, da Immer, amma ba su iya nuna gidajen kakanninsu, ko zuriyarsu a cikin Isra’ilawa ba, su ɗari shida ne da arba’in da biyu.

63 Na wajen firistoci kuma su ne zuriyar Habaya, da na Hakkoz, da na Barzillai, wanda ya auri ‘yar Barzillai mutumin Gileyad, aka kira shi da sunan zuriyar surukinsa.

64 Waɗannan suka nema a rubuta su tare da waɗanda aka rubuta jerin sunayen asalinsu, amma ba a same su a ciki ba, saboda haka aka hana su shiga cikin firistoci, sun zama kamar marasa tsarki.

65 Sai mai mulki ya faɗa musu kada su ci abinci mafi tsarki, sai an sami firist wanda zai yi tambaya ta wurin Urim da Tummin tukuna.

66-69 Jimillar waɗanda suka komo duka su dubu arba’in da dubu biyu da ɗari uku da sittin ne (42,360)

barorinsu mata da maza, waɗanda yawansu ya kai dubu bakwai da ɗari uku da talatin da bakwai (7,337)

mawaƙa ɗari biyu da arba’in da biyar mata da maza

dawakansu kuma ɗari bakwai da talatin da shida ne

alfadaransu kuma ɗari biyu da arba’in da biyar ne

raƙumansu ɗari huɗu da talatin da biyar ne

jakunansu dubu shida da ɗari bakwai da ashirin (6,720)

70-72 Da yawa daga cikin jama’a suka ba da taimako domin biyan aikin gyaran Haikali.

Mai mulki ya ba da

zinariya darik dubu (1,000)

kwanonin wanke hannu guda hamsin

rigunan firistoci ɗari biyar da talatin

Shugabannin iyali suka ba da

zinariya darik dubu ashirin (20,000)

azurfa maina dubu biyu da ɗari biyu (2,200)

Sauran jama’a suka ba da

zinariya darik dubu ashirin (20,000)

azurfa maina dubu biyu (2,000)

rigunan firistoci guda sittin da bakwai

73 Sa’an nan firistoci, da Lawiyawa, da masu tsaron Haikali, da mawaƙa da waɗansu da dama daga cikin jama’a, da ma’aikatan Haikali, da dukan Isra’ilawa suka zauna a garuruwansu.