ZAB 28

Addu’ar Roƙo da Yabo

1 Ina kira gare ka, ya Ubangiji mai kāre ni,

Ka ji kukana!

In kuwa ba ka amsa mini ba,

Zan zama ɗaya daga cikin waɗanda suka gangara zuwa lahira.

2 Ka ji ni lokacin da na yi kuka gare ka neman taimako,

Ina ɗaga hannuwana wajen tsattsarkan Haikalinka.

3 Kada ka kāshe ni tare da mugaye,

Tare da masu aikata mugunta,

Mutane waɗanda maganarsu kamar ta zumunci ce,

Amma zukatansu cike suke da ƙiyayya.

4 Ka hukunta su saboda abin da suka aikata.

Ka hukunta su saboda dukan ayyukansu,

Ka ba su abin da ya cancance su!

5 Ba su kula da abin da Ubangiji ya yi ba,

Ko kuma abin da ya halitta,

Don haka zai hukunta su, ya hallaka su har abada.

6 A yabi Ubangiji,

Gama ya ji kukana na neman taimako!

7 Ubangiji yakan kiyaye ni, yă tsare ni.

Na dogara gare shi.

Ya taimake ni, don haka ina murna,

Ina raira masa waƙoƙin yabo.

8 Ubangiji yana kiyaye jama’arsa,

Yakan kiyaye sarkinsa da ya zaɓa, ya kuma cece shi.

9 Ka ceci jama’arka, ya Ubangiji,

Ka sa wa waɗanda suke naka albarka!

Ka zama makiyayinsu,

Ka lura da su har abada.