ISH 45

Ubangiji ya Mori Sairus

1 Sairus shi ne zaɓaɓɓen sarki na Ubangiji!

Ubangiji ya sa shi ya ci al’ummai,

Ya aike shi ya tuɓe ikon sarakuna,

Ubangiji zai buɗe masa ƙofofin birni.

Ubangiji ya ce wa Sairus,

2 “Ni kaina zan shirya hanya dominka,

Ina baji duwatsu da tuddai.

Zan kakkarye ƙyamaren tagulla,

In kuma daddatse gagara badau na baƙin ƙarfe.

3 Zan ba ka dukiya daga cikin duhu, a asirtattun wurare,

Sa’an nan za ka sani ni ne Ubangiji,

Allah na Isra’ila kuma, shi ne ya zaɓe ka.

4 Na sa ka domin ka taimaki bawana Isra’ila,

Jama’ar da ni na zaɓa.

Na ba ka girma mai yawa,

Ko da yake kai ba ka san ni ba.

5 “Ni ne Ubangiji, ba wani Allah sai ni.

Zan ba ka irin ƙarfin da kake bukata,

Ko da yake kai ba ka san ni ba.

6 Na yi wannan domin dukan waɗanda suke daga wannan bangon duniya zuwa wancan

Su sani ni ne Ubangiji,

Ba kuwa wani Allah sai ni.

7 Ni na halicci haske duk da duhu,

Ni ne na kawo albarka duk da la’ana.

Ni Ubangiji, na yi dukkan waɗannan abu.

8 Zan aiko da nasara daga sararin sama kamar ruwan sama.

Ƙasa za ta buɗe ta karɓe ta,

Za ta kuwa hudo da ‘yanci da gaskiya.

Ni Ubangiji, ni zan sa haka ya faru.”

Ubangiji Mahalicci Ne

9 Ko tukunyar yumɓu tana iya gardama da magininta,

Tukunyar da take daidai da sauran tukwane?

Ko yumɓu ya iya tambayar abin da maginin yake yi?

Ko tukunya tana iya gunaguni a kan magininta?

10 Ko akwai wanda zai iya ce wa iyayensa,

“Don me kuka haife ni kamar haka?”

11 Ubangiji, Allah Mai Tsarki na Isra’ila,

Shi wanda ya halicce su, ya ce,

“Ba ka da iko ka yi mini tambaya game da ‘ya’yana,

Ko ka faɗa mini abin da ya kamata in yi!

12 Ni ne wanda ya halicci duniya,

Na kuma halicci mutum don ya zauna cikinta.

Da ikona na shimfiɗa sammai,

Ina kuwa mallakar rana, da wata, da taurari.

13 Ni kaina na iza Sairus ya yi wani abu,

Don ya cika nufina ya daidaita al’amura.

Zan miƙar da kowace hanyar da zai yi tafiya a kai.

Zai sāke gina birnina, wato Urushalima,

Ya kuma ‘yantar da mutanena da suke bautar talala.

Ba wanda ya yi ijara da shi, ko ya ba shi rashawa don ya yi wannan.”

Ubangiji Mai Runduna ne ya faɗi wannan.

14 Ubangiji ya ce wa Isra’ila,

“Dukiyar Masar da ta Habasha za ta zama taku,

Dogayen mutanen Seba kuma za su zama bayinku,

Za su bi ku suna a ɗaure da sarƙoƙi.

Za su rusuna a gabanku su tuba, su ce,

‘Allah yana tare da ku, shi kaɗai ne Allah.’ ”

15 Allah na Isra’ila, wanda ya ceci mutanensa,

Shi ne yakan ɓoye kansa.

16 Su waɗanda suka yi gumaka, dukansu za su sha kunya,

Dukansu za su zama abin kunya.

17 Amma Ubangiji ya ceci Isra’ila,

Nasararsa kuwa za ta tabbata har abada,

Mutanensa ba za su taɓa shan kunya ba.

18 Ubangiji ne ya halicci sammai,

Shi ne wanda yake Allah!

Shi ne ya shata duniya ya kuma yi ta,

Ya kafa ta, ta kahu da ƙarfi, za ta yi ƙarƙo!

Bai halicce ta hamada da ba kome a ciki ba,

Amma wurin zaman mutane.

Shi ne wanda ya ce, “Ni ne Ubangiji,

Ba kuwa wani Allah, sai ni.

19 Ba a ɓoye na yi magana ba,

Ban kuwa ɓoye nufina ba.

Ban ce jama’ar Isra’ila

Su neme ni a kowace hanyar ruɗami ba.

Ni ne Ubangiji, gaskiya kuwa nake faɗa,

Ina sanar da abin da yake daidai.”

Ubangiji da Gumakan Babila

20 Ubangiji ya ce,

“Ku taru wuri ɗaya ku jama’ar al’ummai,

Dukanku da kuka tsira daga faɗuwar mulki,

Ku gabatar da kanku domin shari’a!

Waɗancan da suka ɗauka gumakansu na itace,

Suna kuma addu’a ga allolin da ba su iya cetonsu,

Waɗannan mutane ba su san kome ba ko kaɗan!

21 Ku zo ku gabatar da matsalarku a ɗakin shari’a,

Bari waɗanda aka kai ƙara su yi shawara da juna.

Wane ne ya faɗi abin da zai faru,

Ya kuma yi annabci tuntuni?

Ashe, ba ni ba ne, Ubangiji, Allah wanda ya ceci mutanensa?

Ba wani Allah sai ni.

22 “Ku juyo wurina a cece ku,

Ku mutane ko’ina a duniya!

Ni kaɗai ne Allah da yake akwai.

23 Abin da na faɗa gaskiya ne,

Ba kuwa zai sāke ba.

Ni, a dukkan yadda nake, na yi alkawari mai ƙarfi,

Kowa da kowa zai zo ya durƙusa a gabana,

Ya yi wa’adin zama mai biyayya a gare ni.

24 “Za su ce ta wurina kaɗai

Za a iya samun nasara da ƙarfi,

Amma dukan waɗanda suka raina ni za su sha kunya.

25 Ni Ubangiji, zan kuɓutar da dukan zuriyar Yakubu,

Za su kuwa yi yabona.”