ISH 50

1 Ubangiji ya ce,

“Kuna tsammani na kori mutanena

Kamar yadda mutum yakan saki mata tasa?

To, in haka ne ina takardar kisan auren?

Kuna tsammani na sayar da ku cikin bauta

Kamar mutumin da ya sayar da ‘ya’yansa?

A’a, kun tafi bauta ne saboda da zunubanku,

Aka tafi da ku saboda da laifofinku.

2 “Don me mutanena ba su amsa ba

Sa’ad da na je wurinsu domin in cece su?

Don me ba su amsa ba sa’ad da na yi kiransu?

Ba ni da isasshen ƙarfin da zan fanshe su ne?

Ina da iko in sa teku ya ƙafe ta wurin umarnina,

Ina kuma da iko in sa rafuffukan ruwa su zama hamada,

Kifayen da suke ciki su mutu saboda rashin ruwa.

3 Ina da iko in sa sararin sama ya yi duhu,

In sa ya zama makoki domin matattu.”

Biyayyar Bawan Ubangiji

4 Ubangiji ya koya mini abin da zan faɗa,

Domin in iya ƙarfafa marar ƙarfi.

A kowace safiya yakan sa in yi marmarin jin abin da zai koya mini.

5 Ubangiji ya ba ni fahimi,

Ban kuwa yi masa tayarwa ba

Ko in juya in rabu da shi.

6 Na tsiraita ga masu dūkana.

Ban hana su sa’ad da suke zagina ba,

Suna tsittsige gemuna,

Suna tofa yau a fuskata.

7 Amma zaginsu ba zai yi mini ƙari ba,

Gama Ubangiji Allah yana taimakona.

Na ƙarfafa kaina domin in jure da su.

Na sani ba zan kunyata ba,

8 Gama Allah yana kusa,

Zai tabbatar da ni, marar laifi ne,

Ko akwai wanda zai iya kawo ƙararraki game da ni?

Bari mu je ɗakin shari’a tare!

Bari ya kawo ƙararrakinsa!

9 Ubangiji kansa zai kāre ni,

Wa zai iya tabbatar da ni mai laifi ne?

Dukan waɗanda suke sarana za su shuɗe,

Za su shuɗe kamar tufar da asu ya cinye!

10 Ku duka da kuke tsoron Ubangiji,

Kuna kuma biyayya da kalmomin bawansa,

Zai yiwu hanyar da kuke bi ta yi duhu ƙwarai,

Amma ku dogara ga Ubangiji, ku jingina ga Allahnku.

11 Dukanku da kuke ƙulle-ƙullen hallaka juna

Ƙulle-ƙullenku za su hallaka ku!

Ubangiji kansa zai sa wannan ya faru,

Za ku gamu da mummunar ƙaddara.