MAT 9

Yesu Ya Warkar da Shanyayye

1 Da ya shiga jirgi, ya haye ya je garinsu.

2 Sai aka kawo masa wani shanyayye, kwance a gado. Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce wa shanyayyen, “Ɗana, ka yi farin ciki, an gafarta maka zunubanka.”

3 Sai waɗansu malaman Attaura suka ce a ransu, “Wannan mutum, ai, saɓo yake!”

4 Yesu kuwa, da yake ya san tunaninsu, ya ce, “Don me kuke mugun tunani a zuciyarku?

5 Wanne ya fi sauƙi, a ce, ‘An gafarta maka zunubanka,’ ko kuwa a ce, ‘Tashi ka yi tafiya’?

6 Amma domin ku sakankance Ɗan Mutum yana da ikon gafarta zunubi a duniya”–sai ya ce wa shanyayyen–“Tashi, ka ɗauki shimfiɗarka ka tafi gida.”

7 Shi kuwa ya tashi ya tafi gida.

8 Da taron suka ga haka, sai tsoro ya kama su, suka ɗaukaka Allah, wanda ya ba mutane iko haka.

Kiran Matiyu

9 Da Yesu ya yi gaba, ya ga wani mutum mai suna Matiyu a zaune, yana aiki a wurin karɓar haraji. Ya ce masa, “Bi ni.” Sai ya tashi ya bi shi.

10 Sa’ad da kuwa Yesu yake cin abinci a gida, sai ga masu karɓar haraji da masu zunubi da yawa sun zo, sun zauna tare da shi da almajiransa.

11 Da Farisiyawa suka ga haka, sai suka ce wa almajiransa, “Don me malaminku yake ci tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?”

12 Amma da Yesu ya ji haka ya ce, “Ai, lafiyayyu ba ruwansu da likita, sai dai marasa lafiya.

13 Sai ku fahimci ma’anar wannan tukuna, ‘Ni kam, zaman jinƙai nake nema a gare ku, ba hadaya ba.’ Ba domin in kira masu adalci na zo ba, sai dai masu zunubi.”

Tambaya a kan Azumi

14 Sai almajiran Yahaya suka zo wurinsa, suka ce, “Don me mu da Farisiyawa mukan yi azumi, amma naka almajiran ba sa yi?”

15 Sai Yesu ya ce musu, “Abokan ango sa yi baƙin ciki tun ango yana tare da su? Ai, lokaci yana zuwa da za a ɗauke musu angon. A sa’an nan ne fa za su yi azumi.

16 Ba mai mahon tsohuwar tufa da sabon ƙyalle, don mahon zai kece tsohuwar tufar, har ma ta fi dā kecewa.

17 Ba kuma mai ɗura sabon ruwan inabi a tsofaffin salkuna. In ma an ɗura, sai salkunan su fashe, ruwan inabin ya zube, salkunan kuma su lalace. Sabon ruwan inabi, ai, sai sababbin salkuna. Ta haka an tserar da duka biyu ke nan.”

‘Yar Shugaban Jama’a da Matar da ta Taɓa Gezar Mayafin Yesu

18 Yana cikin yi musu magana haka, sai ga wani shugaban jama’a ya zo, ya yi masa sujada, ya ce, “Yanzu yanzu ‘yata ta rasu, amma ka zo ka ɗora mata hannu, za ta rayu.”

19 Sai Yesu ya tashi, ya bi shi tare da almajiransa.

20 Ga kuma wata mace wadda ta shekara goma sha biyu tana zub da jini, ta raɓo ta bayansa, ta taɓa gezar mayafinsa,

21 domin ta ce a ranta, “Ko da mayafinsa ma na taɓa, sai in warke.”

22 Sai Yesu ya juya, yă gan ta, ya ce, “’Yata, ki yi farin ciki, bangaskiyarki ta warkar da ke.” Nan take matar ta warke.

23 Da Yesu ya isa gidan shugaban jama’ar, ya kuma ga masu busar sarewa da taro suna ta hayaniya,

24 sai ya ce, “Ku ba da wuri, ai, yarinyar ba matacciya take ba, barci take yi.” Sai suka yi masa dariyar raini.

25 Amma da aka fitar da taron waje, ya shiga ya kama hannunta, sai kuwa yarinyar ta tashi.

26 Wannan labarin kuwa ya bazu a duk ƙasar.

Makafi Biyu Sun Sami Ganin Gari

27 Da Yesu ya yi gaba daga nan, sai waɗansu makafi biyu suka bi shi, suna ɗaga murya suna cewa, “Ya Ɗan Dawuda, ka ji tausayinmu.”

28 Da ya shiga wani gida sai makafin suka zo gare shi. Yesu ya ce musu, “Kun gaskata ina da ikon yin haka?” Sai suka ce masa, “I, ya Ubangiji!”

29 Sa’an nan ya taɓa idanunsu, ya ce, “Yă zama muku gwargwadon bangaskiyarku.”

30 Sai idanunsu suka buɗe. Amma Yesu ya kwaɓe su ƙwarai, ya ce, “Kada fa kowa ya ji labarin.”

31 Amma suka tafi suka yi ta baza labarinsa a duk ƙasar.

Bebe Ya Yi Magana

32 Sun tashi ke nan, sai aka kawo masa wani bebe mai aljan.

33 Bayan an fitar da aljanin, sai beben ya yi magana, taron kuwa suka yi mamaki, suka ce, “Kai! Ba a taɓa ganin irin wannan a cikin Isra’ila ba.”

34 Amma sai Farisiyawa suka ce, “Ai, da ikon sarkin aljannu yake fitar da aljannu.”

Yesu Ya Ji Tausayin Mutane

35 Sai Yesu ya zazzaga dukan garuruwa da ƙauyuka, yana koyarwa a majami’unsu, yana yin bisharar Mulkin Allah, yana kuma warkar da kowace irin cuta da rashin lafiya.

36 Amma da ya ga taro masu yawa sai ya ji tausayinsu, domin suna shan wahala, suna nan a warwatse kamar tumaki da ba makiyayi.

37 Sai ya ce wa almajiransa, “Girbin yana da yawa, amma masu yinsa kaɗan ne.

38 Saboda haka ku roƙi Ubangijin girbin ya turo masu girbi, su yi masa girbi.”