NAH 1

Fushin Ubangiji a kan Nineba

1 Jawabi a kan Nineba ke nan, a littafin wahayin Nahum na Elkosh.

2 Ubangiji Allah mai kishi ne, mai

sakayya,

Ubangiji mai sakayya ne, mai

hasala.

Ubangiji yakan ɗauki fansa a kan

maƙiyansa.

Yana tanada wa maƙiyansa fushi.

3 Ubangiji mai jinkirin fushi ne,

Mai Iko Dukka.

Ubangiji ba zai kuɓutar da mai laifi

ba.

Hanyarsa tana cikin guguwa da cikin

hadiri,

Gizagizai su ne ƙurar ƙafafunsa.

4 Yakan tsauta wa teku, sai teku ta

ƙafe.

Yakan busar da koguna duka.

Bashan da Karmel sukan bushe,

Tohon Lebanon yakan yanƙwane.

5 Duwatsu sukan girgiza a gabansa,

Tuddai kuma su narke.

Duniya ta murtsuke a gabansa,

Da dukan mazauna a cikinta.

6 Wa zai iya tsaya wa fushinsa?

Wa kuma zai iya daurewa da

hasalarsa?

Yana zuba hasalarsa mai kama da

wuta,

Duwatsu sukan farfasu a gabansa.

7 Ubangiji mai alheri ne,

Shi mafaka ne a ranar wahala.

Ya san waɗanda suke fakewa a gare

shi.

8 Zai shafe maƙiyansa da ambaliyar

ruwa,

Zai kuma runtumi maƙiyansa zuwa

cikin duhu.

9 Me kuke ƙullawa game da Ubangiji?

Ubangiji zai wofintar da abin nan da

kuke ƙullawa,

Sau ɗaya kawai zai hallaka ku.

10 Suna maye da abin shansu,

Za su ƙone kamar sarƙaƙƙiyar ƙaya,

Da busasshiyar ciyawa.

11 Daga cikinki wani ya fito,

Wanda ya ƙulla wa Ubangiji

makirci,

Ya ƙulla shawara marar amfani.

12 Ni Ubangiji na ce,

“Ko da yake suna da ƙarfi, suna

kuma da yawa,

Za a datse su, su ƙare.

Ko da yake na wahalar da kai,

Ba zan ƙara wahalar da kai ba.

13 Yanzu zan karya karkiyarsa daga

wuyanka,

Zan kuma tsinke sarƙarta.”

14 Ubangiji ya riga ya yi umarni a

kanka cewa,

“Sunanka ba zai ci gaba ba,

Zan farfashe sassaƙaƙƙun siffofi

Da siffofi na zubi daga gidan

gumakanka.

Zan shirya maka kabari, gama kai

rainanne ne.”

Labarin Fāɗuwar Nineba

15 Duba a kan duwatsu, ƙafafun

wanda yake kawo albishir,

Wanda yake shelar salama!

Ya Yahuza, ka yi bikin idodinka,

Ka kuma cika wa’adodinka.

Gama mugun ba zai sāke zuwa ya yi

gāba da kai ba,

An datse shi ƙaƙaf.