ZAB 64

Addu’ar Neman Tsari

1 Ina shan wahala, ya Allah, ka ji addu’ata!

Ina jin tsoro, ka cece ni daga maƙiyana!

2 Ka kiyaye ni daga ƙulle-ƙullen mugaye,

Da iskancin mugayen mutane.

3 Sukan wasa harsunansu kamar takuba,

Sukan kai bāra da mugayen maganganu kamar kibau.

4 Sukan yi kwanto su harbi mutanen kirki da kibau,

Nan da nan sukan yi harbi, ba su kuwa jin tsoro.

5 Suna ƙarfafa junansu cikin yin mugayen ƙulle-ƙullensu,

Sukan yi ta taɗi a kan inda za su kafa tarkunansu.

“Ba wanda zai gan mu,” in ji su.

6 Sukan shirya maƙarƙashiya, su ce,

“Ai, mun gama shirin aikata laifi sarai.”

Zuciyar mutum da tunaninsa, suna da wuyar ganewa!

7 Amma Allah zai harbe su da kibansa,

Za a yi musu rauni nan da nan.

8 Zai hallaka su saboda maganganunsu,

Duk wanda ya gan su zai kaɗa kansa.

9 Dukansu za su ji tsoro,

Za su faɗi abin da Allah ya aikata,

Su yi tunani a kan ayyukansa.

10 Dukan masu adalci za su yi murna,

Saboda abin da Ubangiji ya aikata.

Za su sami mafaka a gare shi,

Dukan mutanen kirki za su yabe shi.