ZAB 11

Mafakar Adalai

1 Na dogara ga Ubangiji domin zaman lafiya,

Wauta ce idan kun ce mini,

“Ka yi firiya kamar tsuntsu zuwa duwatsu,

2 Domin mugaye sun ja bakkunansu,

Sun kuma ɗana kibansu

Domin su harbi mutanen kirki a duhu.

3 Ba abin da mutumin kirki zai iya yi

Sa’ad da kome ya lalace.”

4 Ubangiji yana cikin tsattsarkan Haikalinsa,

Yana da kursiyinsa a Sama.

Yana kallon dukan mutane

Yana sane da abin da suke yi.

5 Yana auna masu kirki da mugaye dukka,

Yana ƙin marar bin doka gaba ɗaya.

6 Yakan aukar da garwashin wuta

Da kibritu mai cin wuta a kan mugaye,

Yakan hukunta su da harshen wuta mai ƙuna.

7 Ubangiji mai adalci ne, yana ƙaunar kyawawan ayyuka,

Masu yi masa biyayya za su zauna a gabansa.