ZAB 26

Addu’ar Neman Tsare Mutunci

1 Ka hurta rashin laifina, ya Ubangiji,

Gama na yi abin da suke daidai,

Na dogara gare ka gaba ɗaya.

2 Ka jarraba ni ka auna ni, ya Ubangiji,

Ka gwada muradina da tunanina.

3 Madawwamiyar ƙaunarka tana bi da ni,

Amincinka yake yi mini jagora kullayaumin.

4 Ba na tarayya da mutanen banza,

Ba abin da ya gama ni da masu riya.

5 Ina ƙin tarayya da masu mugunta,

Nakan kauce wa mugaye.

6 Ya Ubangiji, na wanke hannuwana

Don in nuna ba ni da laifi,

Da ibada nakan taka, ina kewaya bagadenka.

7 Na raira waƙar godiya,

Na faɗi dukan ayyukanka masu banmamaki.

8 Ya Ubangiji, ina ƙaunar Haikali inda zatinka yake,

Inda ɗaukakarka yake zaune.

9 Kada ka hallaka ni tare da masu zunubi,

Ka cece ni daga ƙaddarar masu kisankai,

10 Mutanen da suke aikata mugunta a dukan lokaci,

A koyaushe suna shirye don su ba da rashawa.

11 Amma ni, ina yin abin da yake daidai,

Ka yi mini jinƙai ka fanshe ni!

12 Na kuɓuta daga dukan hatsarori,

A taron sujada na yabi Ubangiji!