ZAB 8

Ɗaukakar Allah da Martabar Mutum

1 Ya Ubangiji, Ubangijinmu,

An san girmanka ko’ina a dukan duniya.

Yabonka ya kai har sammai,

2 Yara da jarirai suna raira shi,

Ka gina kagara saboda magabtanka,

Domin ka tsai da maƙiyanka da abokan gābanka.

3 Sa’ad da na duba sararin sama, wanda ka yi,

Da wata da taurari waɗanda ka sa a wuraren zamansu,

4 Wane ne mutum, har da kake tunawa da shi,

Mutum kurum, har da kake lura da shi?

5 Duk da haka in banda kai ba wanda ya fi shi,

Ka naɗa shi da daraja da girma!

6 Ka sa shi ya yi mulkin dukan abin da ka halitta,

Ka ɗora shi a kan dukan abubuwa,

7 Tumaki da shanu, har ma da namomin jeji,

8 Da tsuntsaye da kifaye,

Da dukan halittar da suke cikin tekuna.

9 Ya Ubangiji, Ubangijinmu,

An san girmanka ko’ina a dukan duniya!