MIKA 7

Lalacewar Isra’ila

1 Tawa ta ƙare, gama na zama

kamar lokacin da aka gama

tattara amfanin gona,

Kamar lokacin da aka gama kalar

‘ya’yan inabi,

Ba nonon inabi da za a tsinka, a ci,

Ba kuma ‘ya’yan ɓaure da suka

harba wanda raina yake so.

2 Mutanen kirki sun ƙare a duniya,

Ba nagarta a cikin mutane.

Dukansu suna kwanto don su zub da

jini.

Kowa yana farautar ɗan’uwansa da

tarko.

3 Sun himmantu su aikata abin da yake

mugu da hannuwansu.

Sarki da alƙali suna nema a ba su

hanci,

Babban mutum kuma yana faɗar son

zuciyarsa,

Da haka sukan karkatar da zance.

4 Mutumin kirkinsu kamar ƙaya yake,

Mai gaskiyarsu kuwa kamar shingen

ƙaya yake.

Ranar da kuka sa mai tsaro,

A ran nan za a aukar muku da

hukunci.

Yanzu ruɗewarku ta zo,

5 Kada ka dogara ga maƙwabcinka,

Kada kuma ka amince da abokinka.

Ka kuma kame bakinka daga

matarka

Wadda take kwance tare da kai.

6 Gama ɗa yana raina mahaifi,

‘Ya kuma tana tayar wa

mahaifiyarta,

Matar ɗa kuma tana gāba da

surukarta,

Mutanen gidan mutum su ne

maƙiyansa.

Ubangiji Zai Kawo Haske da Ceto

7 Amma ni zan kafa ido ga Ubangiji,

Zan jira ceton Allahna,

Allahna zai ji ni.

8 Ya maƙiyina, kada ka yi murna a

kaina,

Gama sa’ad da na fāɗi, zan tashi

kuma.

Sa’ad da na zauna cikin duhu,

Ubangiji zai haskaka ni.

9 Zan ɗauka fushin Ubangiji ne,

Gama na yi masa zunubi,

Sai lokacin da ya ji da’awata,

Har ya yanke mini shari’a.

Zai kawo ni zuwa wurin haske,

Zan kuwa ga cetonsa.

10 Sa’an nan maƙiyina wanda suke ce mini,

“Ina Ubangiji Allahnka?”

Zai gani, ya kuma ji kunya.

Idanuna za su gan shi lokacin da aka

tattake shi

Kamar taɓo a titi.

11 Za a faɗaɗa iyakarka

A ranar da za a gina garunka.

12 A waccan rana mutane za su zo

wurinka,

Daga Assuriya har zuwa Masar,

Daga Masar zuwa Kogin Yufiretis,

Daga teku zuwa teku, daga dutse

zuwa dutse.

13 Duniya kuwa za ta zama kufai,

Saboda mazaunan da suke cikinta,

Saboda hakkin ayyukansu.

Juyayin Ubangiji a kan Isra’ila

14 Sai ka yi kiwon mutanenka da

sandanka,

Wato garken mallakarka,

Wanda yake zaune shi kaɗai a kurmi

A tsakiyar ƙasa mai albarka.

Bari su yi kiwo cikin Bashan da

Gileyad

Kamar a kwanakin dā.

15 “Zan nuna muku abubuwa masu

banmamaki,

Kamar a kwanakin da kuka fito

ƙasar Masar.”

16 Al’umman duniya za su gani,

Su kuwa ji kunyar ƙarfinsu duka.

Za su sa hannuwansu a baka,

Kunnuwansu za su kurmance.

17 Za su lashi ƙura kamar maciji da

abubuwa masu rarrafe,

Za su fito da rawar jiki daga wurin

maɓuyarsu,

Da tsoro za su juyo wurin Ubangiji

Allahnmu,

Za su ji tsoronka.

18 Akwai wani Allah kamarka, mai yafe

mugunta,

Mai kawar da laifin ringin

gādonsa?

Ba ya riƙon fushi har abada, gama

shi mai alheri ne.

19 Zai sāke jin juyayinmu,

Ya tattake muguntarmu a ƙarƙashin

ƙafafunsa.

Za ka jefar da zunubanmu a cikin

zurfin teku.

20 Za ka nuna wa Yakubu aminci,

Ga Ibrahim kuma madawwamiyar

ƙauna,

Kamar yadda ka rantse wa

kakanninmu

Tun a zamanin dā.