AMOS 2

Mowab

1 Ubangiji ya ce,

“Mutanen Mowab sun ci gaba da

yin zunubi.

Hakika, zan hukunta su,

Don sun ƙone ƙasusuwan Sarkin

Edom

Don su yi toka da su.

2 Zan aukar da wuta a ƙasar

Mowab,

Ta ƙone kagarar Keriyot.

Jama’ar Mowab za su mutu a

hargitsin yaƙi,

Sa’ad da sojoji suke sowa, ana busa

ƙahoni.

3 Zan kashe Sarkin Mowab da

shugabannin ƙasar.”

Yahuza

4 Ubangiji ya ce,

“Mutanen Yahuza sun ci gaba da yin

zunubi.

Hakika, zan hukunta su,

Don sun raina koyarwata sun ƙi

bin umarnaina.

Allolinsu na ƙarya waɗanda

kakanninsu suka bauta wa,

Sun sa su su ratse daga hanya.

5 Saboda haka zan aukar da wuta a

kan Yahuza

Ta ƙone kagarar Urushalima.”

Allah Ya Hukunta Isra’ila

6 Ubangiji ya ce,

“Mutanen Isra’ila sun ci gaba da yin

zunubi.

Hakika, zan hukunta su,

Don sun sayar da salihai waɗanda

suka kāsa biyan bashinsu.

Sun kuma sayar da matalauta

Waɗanda bashinsu bai kai ko kuɗin

bi-shanu ba.

7 Sun tattake marasa ƙarfi da

kāsassu,

Suna tunkuɗe matalauta su wuce.

Tsofaffi da samari sukan tafi wurin

karuwan Haikali.

Ta haka suke ɓata sunana mai

tsarki.

8 A duk wuraren sujadarsu sukan

kwanta

A bisa tufafin da suka karɓe jingina.

A cikin Haikalin Allahnsu, sukan sha

ruwan inabi

Da suka karɓo daga wurin waɗanda

suke bi bashi.

9 “Amma ga shi, saboda ku na

hallakar da Amoriyawa,

Dogayen mutanen nan masu kama

da itatuwan al’ul,

Ƙarfafa kuma kamar itatuwan oak,

Na hallaka su ƙaƙaf.

10 Na fito da ku, wato jama’ata daga

Masar.

Na bi da ku cikin jeji shekara

arba’in,

Na kuwa ba ku ƙasar Amoriyawa ta

zama taku.

11 Na zaɓi waɗansu daga cikin

‘ya’yanku su zama annabawa,

Waɗansu kuma daga cikin samarinku

su zama keɓaɓɓu.

Ko ba haka ba ne, ya ku

Isra’ilawa?

Ni, Ubangiji, na yi magana.

12 Amma kun sa keɓaɓɓu shan ruwan

inabi,

Kuka kuma umarci annabawa kada

su isar da saƙona.

13 Zan danƙare ku a inda kuke

Kamar yadda ake danƙare

amalanke da kayan tsaba.

14 Ko masu saurin gudu ma ba za su

tsere ba,

Ƙarfafa za su zama kumamai,

Sojoji kuma ba za su iya ceton kansu

ba.

15 ‘Yan baka ba za su iya ɗagewa ba.

Masu saurin gudu ba za su tsira ba.

Mahayan dawakai kuma ba za su

tsere da rayukansu ba.

16 Ko sojojin da suka fi jaruntaka duka

ma,

Za su gudu tsirara a ran nan.”

Ubangiji ne ya faɗa.