IRM 10

Gumaka da Allah na Gaskiya

1 Ya jama’ar Isra’ila, ku ji jawabin da Ubangiji yake yi muku.

2 Ubangiji ya ce,

“Kada ku koyi abubuwan da

al’ummai suke yi,

Kada ku ji tsoron alamun da suke a

sama,

Ko da yake al’ummai suna jin

tsoronsu.

3 Gama al’adun mutane na ƙarya ne,

Daga cikin jeji aka sare wani itace,

Gwanin sassaƙa ya sassaƙa shi da

gizago.

4 Mutane sukan yi masa ado na azurfa

da zinariya,

Sukan ɗauki guduma su kafa shi da

ƙusoshi,

Don kada ya motsa.

5 Gumakansu dodon gona suke, a

cikin gonar kabewa,

Ba su iya yin magana,

Ɗaukarsu ake yi domin ba su iya

tafiya!

Kada ku ji tsoronsu.

Gama ba su da ikon aikata mugunta

ko alheri.”

6 Ya Ubangiji, ba wani kamarka,

Kai mai girma ne,

Sunanka kuma yana da girma da

iko.

7 Wane ne ba zai ji tsoronka ba, ya

Sarkin dukan al’ummai?

Ka isa a ji tsoronka,

Gama babu kamarka a cikin dukan

masu hikima na al’ummai,

Da kuma cikin dukan mulkokinsu,

Ba wani kamarka.

8 Dukansu dakikai ne wawaye,

Koyarwar gumaka ba wani abu ba

ne, itace ne kawai!

9 An kawo fallayen azurfa daga

Tarshish,

Da zinariya kuma daga Ufaz,

Aikin gwanaye da maƙeran

zinariya.

Tufafinsu na mulufi ne da shunayya,

duka aikin gwanaye.

10 Amma Ubangiji shi ne Allah na

gaskiya,

Shi Allah mai rai ne,

Shi Sarki ne madawwami.

Saboda hasalarsa duniya ta girgiza,

Al’ummai ba za su iya jurewa da

fushinsa ba.

11 Haka za ku faɗa musu, “Gumakan da ba su yi sammai da duniya ba, za su lalace a duniya da a ƙarƙashin sammai.”

12 Shi ne, ta wurin ikonsa ya yi duniya,

Ta wurin hikimarsa ya kafa ta,

Ta wurin basirarsa kumaya ya shimfiɗa

sammai.

13 Sa’ad da ya yi murya akan ji ƙugin

ruwa a cikin sammai

Yakan kawo ƙasashi daga ƙurewar

duniya,

Yakan yi walƙiyoyi saboda ruwan

sama,

Daga cikin taskokinsa yakan kawo

iska.

14 Kowane mutum dakiki ne, marar

ilimi,

Kowane maƙerin zinariya zai sha

kunya saboda gumakansa,

Gama siffofinsa ƙarya ne,

Ba numfashi a cikinsu.

15 Su ba kome ba ne, aikin ruɗami ne,

A lokacin da za a hukunta su za su

lalace.

16 Gama shi ba kamar waɗannan yake

ba,

Shi na Yakubu ne.

Shi ne ya yi dukan kome,

Kabilan Isra’ilawa gādonsa,

Sunansa Ubangiji Mai Runduna.

Risɓewar Yahuza

17 Ku tattara kayayyakinku,

Ku mazaunan wurin da aka kewaye

da yaƙi.

18 Gama haka Ubangiji ya ce,

“Ga shi, ina jefar da mazaunan

ƙasar daga ƙasarsu a wannan

lokaci,

Zan kawo musu wahala, za su kuwa

ji jiki.”

19 Tawa ta ƙare, saboda raunin da aka

yi mini.

Raunina mai tsanani ne,

Amma na ce, lalle wannan azaba ce,

Tilas in daure da ita.

20 An lalatar da alfarwata,

Dukan igiyoyi sun tsintsinke,

‘Ya’yana maza sun bar ni, ba su

nan.

Ba wanda zai kafa mini alfarwata

Ya kuma rataya labulena.

21 Makiyayan dakikai ne,

Ba su roƙi Ubangiji ba,

Don haka ba su sami wadata ba,

An watsa dukan garkensu.

22 Ku ji fa, an ji ƙishin-ƙishin! Ga shi

kuma, yana tafe.

Akwai babban hargitsin da ya fito

daga arewa,

Don a mai da biranen Yahuza kufai,

wurin zaman diloli.

23 “Ya Ubangiji, na sani al’amuran

mutum ba a hannunsa suke ba,

Ba mutum ne yake kiyaye takawarsa

ba

24 Ka tsauta mini, ya Ubangiji, amma

da adalcinka,

Ba da fushinka ba, don kada ka

wofinta ni.

25 Ka kwarara hasalarka a kan sauran

al’umma da ba su san ka ba,

Da a kan jama’ar da ba su kiran

sunanka,

Gama sun cinye Yakubu,

Sun cinye shi, sun haɗiye shi,

Sun kuma mai da wurin zamansa

kufai.”