IRM 9

1 Da ma kaina ruwa ne kundum,

Idanuna kuma maɓuɓɓuga ne,

Da sai in yi ta kuka dare da rana,

Saboda an kashe jama’ata!

2 Da ma ina da wurin da zan fake a

hamada,

Da sai in rabu da mutanena, in tafi

can!

Gama dukansu mazinata ne,

Ƙungiyar mutane maciya amana.

3 Ubangiji ya ce,

“Sun tanƙwasa harshensu kamar

baka,

Ƙarya ce take rinjayar gaskiya a

ƙasar.

Suna ta cin gaba da aikata mugunta,

Ba su kuwa san ni ba.

4 “Bari kowane mutum ya yi hankali

da maƙwabcinsa,

Kada kuma ya amince da kowane

irin ɗan’uwa,

Gama kowane ɗan’uwa munafuki

ne,

Kowane maƙwabci kuma mai kushe

ne.

5 Kowane mutum yana ruɗin

maƙwabcinsa da abokinsa,

Ba mai faɗar gaskiya,

Sun koya wa harshensu faɗar

ƙarya.

Suna aikata laifi,

Sun rafke, sun kasa tuba.

6 Suna ƙara zalunci a kan zalunci,

Yaudara a kan yaudara,

Sun ƙi sanina,” in ji Ubangiji.

7 Saboda haka, Ubangiji Mai

Runduna, ya faɗa cewa,

“Zan tsabtace su, in gwada su,

Gama me zan yi kuma saboda

jama’ata?

8 Harshensu kibiya ce mai dafi, yana

faɗar ƙarya,

Kowa yana maganar alheri da

maƙwabcinsa

Amma a zuciyarsa yana shirya masa

maƙarƙashiya.

9 Ba zan hukunta su saboda waɗannan

al’amura ba?

Ba zan sāka wa al’umma irin

wannan ba?”

10 Zan yi kuka in yi kururuwa saboda

tsaunuka,

Zan yi kuka saboda wuraren kiwo,

Domin sun bushe sun zama marasa

amfani.

Ba wanda yake bi ta cikinsu.

Ba a kuma jin kukan shanu,

Tsuntsaye da namomin jeji, sun gudu

sun tafi.

11 “Ni Ubangiji na ce, zan mai da

Urushalima tsibin kufai,

Wurin zaman diloli,

Zan kuma mai da biranen Yahuza

kufai, inda ba kowa.”

Za a Rushe Birni a Kai su Zaman Talala

12 Wa yake da isasshiyar hikimar da zai fahimci wannan? Wa Ubangiji ya faɗa masa don ya sanar? Me ya sa ƙasar ta lalace ta zama kufai, har ba wanda yake iya ratsa ta, kamar hamada?

13 Sai Ubangiji ya ce, “Saboda sun bar dokata wadda na sa a gabansu, ba su yi biyayya da maganata ko su yi aiki da ita ba.

14 Amma suka taurare, suka biye wa zuciyarsu, suka bi Ba’al, kamar yadda kakanninsu suka koya musu.

15 Domin haka, ni Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila, zan ciyar da mutanen nan da abinci mai ɗaci, in shayar da su da ruwan dafi.

16 Zan watsa su cikin sauran al’umma waɗanda su da kakanninsu ba su san su ba, zan sa takobi ya bi su don in hallaka su.

17 “Haka ni Ubangiji Mai Runduna na

ce,

Ku yi tunani, ku kirawo mata masu

makoki su zo,

Ku aika wa gwanaye fa.”

18 Jama’a suka ce,

“Su gaggauta, su ta da murya,

Su yi mana kuka da ƙarfi,

Har idanunmu su cika da hawaye,

Giranmu kuma su jiƙe sharaf.

19 “Gama ana jin muryar kuka daga

Sihiyona cewa,

‘Ga yadda muka lalace! Aka kunyatar

da mu ɗungum!

Don mun bar ƙasar, domin sun

rurrushe wuraren zamanmu.’ ”

20 Irmiya ya ce,

“Ya ku mata, ku ji maganar

Ubangiji,

Ku kasa kunne ga maganar da ya

faɗa,

Ku koya wa ‘ya’yanku mata kukan

makoki,

Kowacce ta koya wa maƙwabciyarta

waƙar makoki,

21 Gama mutuwa ta shiga tagoginmu,

Ta shiga cikin fādodinmu,

Ta karkashe yara a tituna,

Ta kuma karkashe samari a dandali.

22 Ubangiji ya ce mini,

‘Ka yi magana, cewa gawawwakin

mutane za su fāɗi tuli

Kamar juji a saura,

Kamar dammunan da masu girbi

suka ɗaura,

Ba wanda zai tattara su.’ ”

23 Ubangiji ya ce, “Kada mai hikima ya yi fariya da hikimarsa, kada mai ƙarfi ya yi fariya da ƙarfinsa, kada kuma mawadaci ya yi fariya da wadatarsa.

24 Amma bari wanda zai yi fariya, ya yi fariya a kan cewa ya fahimce ni, ya kuma san ni. Ni ne Ubangiji mai yin alheri, da gaskiya, da adalci a duniya, gama ina murna da waɗannan abubuwa, ni Ubangiji na faɗa.”

25 Ubangiji ya ce, “Kwanaki suna zuwa sa’ad da zan hukunta dukan waɗanda aka yi musu kaciya,

26 da Masar, da Yahuza, da Edom, da ‘ya’yan Ammon, maza, da na Mowab, da dukan waɗanda suke zaune a hamada, da waɗanda suke yi wa kansu sanƙo, gama dukan al’umman nan marasa kaciya ne, dukan jama’ar Isra’ila kuma marasa kaciya ne a zuci.”