IRM 8

1 “Ni Ubangiji na faɗa, cewa a wancan lokaci, za a fitar da ƙasusuwa daga kaburburan sarakunan Yahuza, da na sarakansu, da na firistoci, da na annabawa, da na mazaunan Urushalima.

2 Za a shimfiɗa su a rana, da a farin wata, da a gaban dukan rundunan sama, waɗanda suka ƙaunata, suka bauta wa, waɗanda suka nemi shawararsu, suka yi musu sujada. Ba za a tattara su a binne ba, amma za su zama juji a bisa ƙasa.

3 Sauran mutanen muguwar tsaran nan waɗanda suke a wuraren da na warwatsa su, za su fi son mutuwa fiye da rayuwa. Ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa.”

Zunubi da Hukunci

4 “Ka faɗa musu, ka ce, ni Ubangiji na

ce,

‘Wanda ya fāɗi ba zai sāke tashi ba?

Idan wani ya kauce ba zai komo kan

hanya ba?

5 Me ya sa, mutanen nan na

Urushalima suke ratsewa, suke

komawa baya kullayaumin?

Sun riƙe ƙarya kan-kan

Sun ƙi komowa.

6 Na kula sosai, na saurara,

Amma ba wanda ya faɗi wata

maganar kirki,

Ba wanda ya taɓa barin muguntarsa,

Kowa cewa yake, “Me na yi?”

Kamar dokin da ya kutsa kai cikin

fagen fama.

7 Ko shamuwa ta sararin sama ma, ta

san lokatanta,

Tattabara da tsattsewa, da gauraka

suna kiyaye lokacin komowarsu.

Amma mutanena ba su san dokokina

ba.

8 Ƙaƙa za ku ce, “Muna da hikima,

Dokar Ubangiji tana tare da mu”?

Ga shi kuwa, alkalamin ƙarya na

magatakarda, ya yi ƙarya.

9 Za a kunyatar da masu hikima.

Za su tsorata, za a kuma tafi da su.

Ga shi, sun ƙi maganar Ubangiji.

Wace hikima suke da ita?

10 Saboda haka zan ba da matansu ga

waɗansu,

Gonakinsu kuma ga waɗanda suke

cinsu da yaƙi,

Saboda tun daga ƙarami har zuwa

babba

Kowannensu yana haɗamar cin

muguwar riba,

Tun daga annabawa zuwa firistoci

Kowannensu aikata ha’inci yake yi.

11 Sun warkar da raunin mutanena

sama sama,

Suna cewa, “Lafiya, lafiya,” alhali

kuwa ba lafiya.

12 Ko sun ji kunya

Sa’ad da suka aikata ayyuka masu

banƙyama?

A’a, ba su ji kunya ba ko kaɗan,

Fuskarsu ko gezau ba ta yi ba.

Domin haka za su faɗi tare da

fāɗaɗɗu,

Sa’ad da na hukunta su, za a ci su da

yaƙi.

Ni Ubangiji na faɗa.’

13 “Ni Ubangiji na ce,

‘Sa’ad da zan tattara su kamar

amfanin gona,

Sai na tarar ba ‘ya’ya a kurangar

inabi,

Ba ‘ya’ya kuma a itacen ɓaure,

Har ganyayen ma sun bushe.

Abin da na ba su kuma ya kuɓuce

musu.

Ni Ubangiji na faɗa.’ ”

14 Mutanen Urushalima sun ce,

“Don me muke zaune kawai?

Bari mu tattaru, mu tafi cikin

garuruwa masu garu,

Mu mutu a can,

Gama Ubangiji Allahnmu ya

ƙaddara mana mutuwa,

Ya ba mu ruwan dafi,

Domin mun yi masa laifi.

15 Mun sa zuciya ga salama, amma ba

lafiya,

Mun sa zuciya ga lokacin samun

warkewa,

Amma sai ga razana!

16 Daga Dan, an ji firjin dawakai.

Dakan ƙasar ta girgiza saboda

haniniyar ingarmunsu.

Sun zo su cinye ƙasar duk da abin

da suke cikinta,

Wato da birnin da mazauna

cikinsa.”

17 “Ni Ubangiji na ce, ‘Zan aiko muku

da macizai, da kāsā,

Waɗanda ba su da makari,

Za su sassare ku.’ ”

18 Baƙin cikina ya fi ƙarfin warkewa,

Zuciyata ta ɓaci ƙwarai!

19 Ku ji kukan jama’ata ko’ina a

ƙasar,

“Ubangiji, ba shi a Sihiyona

ne?

Sarkinta ba ya a cikinta ne?”

Ubangiji ya ce,

“Me ya sa suka tsokane ni da

sassaƙaƙƙun gumakansu,

Da baƙin gumakansu?”

20 Mutane suna ta cewa,

“Damuna ta ƙare, kaka kuma ta

wuce,

Amma ba a cece mu ba.”

21 Raunin da aka yi wa jama’ata,

Ya yi wa zuciyata rauni.

Ina makoki, tsoro kuma ya kama ni

ƙwarai.

22 Ba abin sanyayawa a Gileyad ne?

Ba mai magani a can ne?

Me ya sa ba a warkar da jama’ata

ba?