IRM 4

1 Ubangiji ya ce,

“Ya mutanen Isra’ila, idan za ku

juyo ku komo wurina,

Idan kuka kawar da abubuwan

banƙyama daga gabana,

Kuka kuma bar yin shakka,

2 Idan kun yi rantsuwa kuka ce,

‘Har da ran Ubangiji kuwa,‘

Da gaskiya, da aminci, da adalci,

Sa’an nan sauran al’umma za su so

in sa musu albarka,

Za su kuma yabe ni.”

3 Ubangiji ya ce wa mutanen Yahuza da na Urushalima,

“Ku kafce saurukanku,

Kada ku yi shuka cikin ƙayayuwa.

4 Ya ku mutanen Yahuza da na

Urushalima,

Ku yi wa kanku kaciya domin

Ubangiji,

Ku kawar da loɓar zukatanku

Don kada fushina ya fito kamar

wuta,

Ya cinye, ba mai iya kashewa,

Saboda mugayen ayyukan da kuka

aikata.”

Yahuza tana cikin Barazanar Yaƙi

5 “Ku yi shela a cikin Yahuza,

Ku ta da murya a Urushalima, ku

ce,

‘Ku busa ƙaho a dukan ƙasar!’

Ku ta da murya da ƙarfi, ku ce,

‘Ku tattaru, mu shiga birane masu

garu.’

6 Ku ta da tuta wajen Sihiyona!

Ku sheƙa a guje neman mafaka,

kada ku tsaya!

Gama zan kawo masifa da babbar

halaka daga arewa.

7 Zaki ya hauro daga cikin

ruƙuƙinsa,

Mai hallaka al’ummai ya kama

hanya,

Ya fito daga wurin zamansa don ya

mai da ƙasarku kufai,

Ya lalatar da biranenku, su zama

kango, ba kowa.

8 Domin haka sai ku sa tufafin

makoki,

Ku yi makoki ku yi kuka,

Gama fushin Ubangiji bai rabu da

mu ba.”

9 Ubangiji ya ce, “A ranan nan, sarki da sarakuna, za su rasa ƙarfin hali, firistoci za su firgita, annabawa kuwa za su yi mamaki.”

10 Sai na ce, “Kaito, kaito, ya Ubangiji Allah, ka ruɗi jama’an nan da Urushalima, da ka ce musu, ‘Za ku zauna lafiya,’ amma ga shi, takobi zai sassare su.”

11 Lokaci yana zuwa da za a faɗa wa mutanen Urushalima cewa, “Iska mai zafi za ta huro daga tuddan hamada zuwa wajen jama’ata, ba domin a sheƙe ta ko a rairaye ta ba!

12 Wannan iska da za ta zo daga wurin Ubangiji, tana da mafificin ƙarfi. Yanzu fa zan yanke hukunci a kansu.”

Abokan Gāba sun Kewaye Yahuza da Yaƙi

13 Duba, ga abokin gāba yana zuwa

kamar gizagizai,

Karusan yaƙinsa suna kama da

guguwa,

Dawakansa sun fi gaggafa sauri.

Kaitonmu, mun shiga uku!

14 Ya Urushalima, ki wanke mugunta

daga zuciyarki,

Domin a cece ki,

Har yaushe mugayen tunaninki za su

yi ta zama a cikinki?

15 Gama wata murya daga Dan ta

faɗa,

Ta kuma yi shelar masifar da za ta

fito daga duwatsun Ifraimu.

16 “A faɗakar da al’ummai, yana zuwa,

A faɗa wa Urushalima cewa,

‘Masu kawo mata yaƙi suna zuwa

daga ƙasa mai nisa,

Suna yi wa biranen Yahuza ihu.

17 Za su kewaye Yahuza kamar masu

tsaron saura,

Saboda ta tayar wa Ubangiji.’ Ni

Ubangiji na faɗa.

18 “Al’amuranki da ayyukanki suka

jawo miki wannan halaka,

Tana da ɗaci kuwa,

Ta soki har can cikin zuciyarki.”

Irmiya ya yi Baƙin Ciki don Mutanensa

19 Azaba! Ba zan iya daurewa da azaba

ba!

Zuciyata! Gabana yana faɗuwa da

ƙarfi,

Ba zan iya yin shiru ba,

Gama na ji amon ƙaho da hargowar

yaƙi.

20 Bala’i a kan bala’i,

Ƙasa duka ta zama kufai,

An lalatar da alfarwaina, ba zato ba

tsammani,

Labulena kuwa farat ɗaya.

21 Har yaushe zan yi ta ganin tuta,

In yi ta jin amon ƙaho?

22 Ubangiji ya ce,

“Mutanena wawaye ne,

Ba su san ni ba,

Yara ne dakikai,

Ba su da ganewa.

Suna gwanance da aikin mugunta,

Amma ba su san yadda za su yi

nagarta ba.”

23 Da na duba duniya sai na ga kufai ce

kawai ba kome,

Na kuma dubi sammai sai na ga ba

haske.

24 Da na duba duwatsu, sai na ga suna

makyarkyata,

Dukan tuddai kuma suna rawar jiki,

su yi gaba su yi baya.

25 Na duba sai na ga ba ko mutum

ɗaya,

Dukan tsuntsaye kuma sun tsere.

26 Na duba, sai na ga ƙasa mai dausayi

ta zama hamada,

An mai da dukan biranenta

kangwaye

A gaban Ubangiji saboda zafin

fushinsa.

27 Gama Ubangiji ya ce, “Ƙasar duka za ta zama kufai, amma duk da haka, ba wannan ne zai zama ƙarshenta na har abada ba.

28 Duniya za ta yi makoki saboda

wannan,

Sammai za su duhunta,

Gama ni na faɗa, haka kuwa na nufa

in yi,

Ba zan ji tausayi ba,

Ba zan kuwa fāsa ba.”

29 Da jin motsin mahayan dawakai da

na maharba

Kowane gari zai fashe.

Waɗansu za su shiga kurama,

Waɗansu kuma su hau kan duwatsu.

Dukan birane za su fashe tas,

Ba wanda zai zauna a cikinsu.

30 Ya ke da kike kufai marar kowa,

Me kike nufi da kika ci ado da mulufi,

Kike caɓa ado da kayan zinariya,

Kika sa wa idanunki tozali ram?

Kin yi kwalliyarki a banza,

Abokan sha’anin karuwancinki sun

raina ki,

Ranki suke nema.

31 Na ji kuka kamar na mace wadda take

naƙuda,

Na ji nishi kamar na mace a lokacin

haihuwarta ta fari,

Na ji kukan ‘yar Sihiyona tana

kyakyari,

Tana miƙa hannuwanta tana cewa,

“Wayyo ni kaina, gama ina suma a

gaban masu kisankai!”