IRM 5

Zunubin Urushalima da Yahuza

1 “Ku bi titunan Urushalima ko’ina!

Ku dudduba ku lura!

Ku bincika kowane dandali, ku gani,

Ko za ku iya samun ko mutum ɗaya

Mai aikata adalci, mai son gaskiya,

Sai in gafarta mata.

2 Ko da yake suna cewa, ‘Na rantse da

ran Ubangiji,’

Duk da haka rantsuwar ƙarya suke

yi.”

3 Ya Ubangiji, ashe, ba masu gaskiya

kake so ba?

Ka buge su, amma ba su yi nishi ba,

Ka hore su, amma sun ƙi horuwa,

Fuskarsu ta ƙeƙashe fiye da dutse,

Sun ƙi tuba.

4 Sai na ce,

“Waɗannan mutane ba su da kirki,

Ba su da hankali,

Ba su san hanyar Ubangiji,

Ko shari’ar Allahnsu ba.

5 Zan tafi wurin manyan mutane, in yi

musu magana,

Gama sun san nufin Ubangiji, da

shari’ar Allahnsu.”

Amma dukansu sun ƙi yarda

Ubangiji ya mallake su,

Suka ƙi yi masa biyayya.

6 Domin haka zaki daga kurmi zai

kashe su,

Kyarkeci kuma daga hamada zai

hallaka su.

Damisa tana yi wa biranensu

kwanto,

Duk wanda ya fita daga cikinsu sai a

yayyage shi,

Domin laifofinsu sun yi yawa,

Karkacewarsu babba ce.

7 “Don me zan gafarce ki?

‘Ya’yanki sun rabu da ni,

Sun yi rantsuwa da gumaka,

Na ciyar da su har sun ƙoshi sosai,

Suka yi karuwanci, suka ɗunguma

zuwa gidajen karuwai,

8 Kamar ƙosassun ingarmu suke,

masu jaraba,

Kowa yana haniniya, yana neman

matar maƙwabcinsa.

9 Ba zan hore su saboda waɗannan

abubuwa ba?

Ni Ubangiji na ce, ba zan ɗauka wa

kaina fansa a kan wannan

al’umma ba?

10 Ku haura, ku lalatar da gonar

kurangar inabinta,

Amma kada ku yi mata ƙarƙaf,

Ku sassare rassanta,

Gama su ba na Ubangiji ba ne.

11 Gama mutanen Isra’ila da mutanen

Yahuza

Sun zama marasa aminci a gare ni.

Ni Ubangiji na faɗa.”

12 Sun yi ƙarya a kan Ubangiji,

Suka ce, “Ba abin da zai yi,

Ba wata masifa da za ta same mu.

Ba kuwa za mu ga takobi ko yunwa

ba.

13 Annabawa holoƙo ne kawai,

Maganar ba ta cikinsu.

Haka za a yi da su!”

Urushalima tana gab da Faɗuwa

14 Saboda haka Ubangiji Allah Mai

Runduna ya ce,

“Domin sun hurta wannan magana,

Ga shi, zan sa maganata a bakinka ta

zama wuta,

Waɗannan mutane kuwa su zama

itace,

Wutar za ta cinye su.

15 “Ya ku mutanen Isra’ila, ga shi, ina

kawo muku

Wata al’umma daga nesa,” in ji

Ubangiji,

“Al’umma ce mai ƙarfin hali ta tun

zamanin dā.

Al’umma wadda ba ku san harshenta

ba,

Ba za ku fahimci abin da suke faɗa

ba.

16 Kwarinsu kamar buɗaɗɗen kabari

ne,

Dukansu jarumawa ne.

17 Za su cinye amfanin gonakinku da

abincinku.

Za su ƙare ‘ya’yanku mata da maza.

Za su cinye garkunanku na tumaki,

da na awaki, da na shanu,

Za su kuma cinye ‘ya’yan inabinku

da na ɓaurenku.

Za su hallaka biranenku masu kagara

da takobi, waɗanda kuke fariya da

su.

18 “Amma ko a cikin waɗancan kwanaki ba zan yi muku ƙaƙaf ba,” in ji Ubangiji.

19 “Sa’ad da mutanenki suka ce, ‘Me ya sa Ubangiji Allahnmu ya yi mana waɗannan abubuwa duka?’ sai ki ce musu, ‘Kamar yadda kuka rabu da ni kuka bauta wa gumaka a ƙasarku, haka kuma za ku bauta wa baƙi a ƙasar da ba taku ba.’ ”

20 “Ka sanar wa zuriyar Yakubu da

wannan,

Ka kuma yi shelarsa a Yahuza, ka

ce,

21 ‘Ku ji wannan, ya ku wawaye,

marasa hankali,

Kuna da idanu, amma ba ku gani,

Kuna da kunnuwa, amma ba ku

ji.’ ”

22 Ubangiji ya ce, “Ba za ku ji tsorona

ba?

Ba za ku yi rawar jiki a gabana ba?

Ni ne na sa yashi ya zama iyakar

teku,

Tabbatacciyar iyaka, wadda ba ta

hayuwa,

Ko da yake raƙuman ruwa za su yi

hauka, ba za su iya haye ta ba,

Ko da suna ruri, ba za su iya wuce ta

ba.

23 Amma mutanen nan suna da taurin

zuciya, masu halin tayarwa ne,

Sun rabu da ni, sun yi tafiyarsu.

24 A zuciya ba su cewa,

‘Bari mu ji tsoron Ubangiji

Allahnmu

Wanda yake ba mu ruwan sama a

kan kari,

Na kaka da na bazara,

Wanda yake ba mu lokacin girbi.’

25 Laifofinku sun raba ku da waɗannan

abubuwa.

Zunubanku kuma sun hana ku

samun alheri.

26 “Gama an sami mugaye, a cikin

jama’ata,

Suna kwanto kamar masu kafa

ashibta.

Sun ɗana tarko su kama mutane.

27 Kamar kwando cike da tsuntsaye,

Haka nan gidajensu suke cike da cin

amana,

Don haka suka zama manya, suka

sami dukiya.

28 Sun yi ƙiba, sun yi bul-bul,

Ba su da haram a kan aikata

mugunta,

Ba su yi wa marayu shari’ar adalci,

don kada su taimake su.

A wajen shari’a ba su bin hakkin

matalauta.

29 “Ba zan hukunta su saboda

waɗannan abubuwa ba?

Ba zan ɗaukar wa kaina fansa a kan

al’umma irin wannan ba?

30 “Abin banmamaki da bantsoro

Ya faru a ƙasar.

31 Annabawa sun yi annabcin ƙarya,

Firistoci kuma sun yi mulki da ikon

kansu,

Mutanena kuwa suna so haka!

Amma sa’ad da ƙarshe ya zo, me za

ku yi?”