IRM 6

Ajalin Urushalima da Yahuza

1 “Ya ku mutanen Biliyaminu, ku

gudu neman mafaka,

Daga cikin Urushalima!

Ku busa ƙaho a Tekowa,

Ku ba da alama a Bet-akkerem,

Gama masifa da babbar halaka sun

fito daga arewa.

2 Ya Sihiyona, ke kyakkyawar

makiyaya ce, zan hallaka abin da

kika hahhaifa.

3 Makiyaya da garkunansu za su zo

wurinki,

Za su kafa alfarwansu kewaye da ke,

Kowa zai yi kiwo a makiyayarki.

4 Za su ce, ‘Mu yi shiri mu fāɗa mata

da yaƙi!

Ku tashi, mu fāɗa musu da tsakar

rana!’

Sai kuma suka ce, ‘Kaitonmu, ga

rana tana faɗuwa, ta yi ruɗa-

kuyangi.

5 Mu tashi mu fāɗa mata da dare,

Mu lalatar da fādodinta.’ ”

6 Ubangiji Mai Runduna ya ce,

“Ku sassare itatuwanta,

Ku tula ƙasa kewaye da

Urushalima,

Dole in hukunta wannan birni

saboda ba kome cikinsa sai

zalunci,

7 Kamar yadda rijiya take da ruwa

garau,

Haka Urushalima take da

muguntarta,

Ana jin labarin kama-karya da na

hallakarwa a cikinta,

Kullum akwai cuce-cuce, da raunuka

a gabana,

8 Ku ji faɗaka, ya ku mutanen

Urushalima,

Don kada a raba ni da ku,

Don kada in maishe ku kufai,

Ƙasar da ba mazauna ciki.”

9 Ubangiji Mai Runduna ya ce,

“Za a kalace ringin Isra’ila sarai,

kamar yadda ake wa inabi,

Ka miƙa hannunka a kan rassanta

kamar mai tsinkar ‘ya’yan

inabi.”

10 Da wa zan yi magana don in faɗakar

da shi, don su ji?

Ga shi, kunnuwansu a toshe suke, su

ji,

Ga shi, maganar Ubangiji kuwa ta

zama abin ba’a a gare su,

Ba su marmarinta.

11-12 Don haka ina cike da fushin

Ubangiji

Na gaji da kannewa.

Ubangiji ya ce,

“Zan kwararo fushi kan yara da suke a

titi.

Da kuma kan tattaruwar samari.

Za a ɗauke mata da miji duka biyu,

Da tsofaffi, da waɗanda suka tsufa

tukub-tukub.

Za a ba waɗansu gidajensu, da

gonakinsu, da matansu,

Gama zan nuna ikona in hukunta

mazaunan ƙasar.

13 Gama daga ƙaraminsu zuwa babba,

Kowannensu yana haɗama ya ci

ƙazamar riba,

Har annabawa da firistoci,

Kowannensu ya shiga aikata rashin

gaskiya.

14 Sun warkar da raunin mutanena

sama sama,

Suna cewa, ‘Lafiya, Lafiya,’ alhali

kuwa ba lafiya.

15 Sun ji kunya sa’ad da suka aikata

abubuwan banƙyama?

Ba su ji kunya ba ko kaɗan.

Ko gezau ba su yi ba,

Don haka za su fāɗi tare da

fāɗaɗɗu,

Sa’ad da na hukunta su, za a

hamɓarar da su.

Ni Ubangiji na faɗa.”

16 Haka Ubangiji ya ce,

“Ku tsaya kan hanyoyi, ku duba,

Ku nemi hanyoyin dā, inda hanya

mai kyau take,

Ku bi ta, don ku hutar da

rayukanku.

Amma suka ce, ‘Ai, ba za mu bi ta ba.’

17 Na sa muku matsara cewa, in kun ji

an busa ƙaho ku kula!

Amma suka ce, ‘Ba za mu kula ba.’

18 “Don haka, ku ji, ya ku al’ummai,

Ku sani, ku taron jama’a,

Don ku san abin da zai same ku.

19 Ki ji, ya ke duniya,

Ga shi, ina kawo masifa a kan

wannan jama’a,

Sakayyar ƙulle-ƙullensu,

Don ba su kula da maganata ba,

Sun ƙi dokokina.

20 Da wane nufi kuke kawo mini turare

daga Sheba,

Ko raken da kuke kawowa daga

ƙasa mai nisa?

Ba zan karɓi hadayunku na ƙonawa

ba,

Ba kuwa zan ji daɗin sadakokinku

ba.

21 Don haka, ni Ubangiji na ce,

Zan sa abin tuntuɓe a gaban wannan

jama’a,

Za su kuwa yi tuntuɓe, su fāɗi.

Iyaye tare da ‘ya’yansu, da

maƙwabci,

Do abokansu za su lalace.”

22 Haka Ubangiji ya ce,

“Ga shi, jama’a tana fitowa daga

ƙasar arewa.

Babbar al’umma ce,

Ta yunƙuro tun daga manisantan

wurare na duniya.

23 Suna riƙe da baka da māshi,

Mugaye ne marasa tausayi,

Motsinsu kamar ƙugin teku ne.

Suna haye a kan dawakai,

A jere kamar wanda ya yi shirin

yaƙi

Gāba da ke, ya ‘yar Sihiyona.”

24 Mutanen Urushalima sun ce,

“Mun ji labarin yaƙin,

Hannuwanmu suka yi rauni.

Azaba ta kama mu,

Ciwo irin na mai naƙuda.

25 Kada ku fita zuwa gona,

Kada kuma ku yi yawo a kan

hanya,

Gama abokin gāba yana da takobi,

Razana a kowane sashi.”

26 “Ya mutanena, ku sa tufafin makoki,

Ku yi birgima cikin toka,

Ku yi makoki mai zafi irin wanda

akan yi wa ɗa tilo,

Gama mai hallakarwa zai auko mana

nan da nan.”

27 Ubangiji ya ce wa Irmiya,

“Na maishe ka mai aunawa da mai

jarraba mutanena

Domin ka sani, ka auna

al’amuransu,

28 Su duka masu taurinkai ne, ‘yan

tawaye,

Suna yawo suna baza jita-jita.

Su tagulla ne da baƙin ƙarfe,

Dukansu lalatattu ne.

29 Ana zuga da ƙarfi,

Dalma ta ƙone,

Tacewar aikin banza ne,

Gama ba a fitar da mugaye ba.

30 Ana ce da su ƙwan maƙerar azurfa

ne,

Gama ni na ƙi su.”