IRM 49

Jawabin Ubangiji a kan Ammonawa

1 Wannan shi ne abin da Ubangiji ya faɗa akan Ammonawa,

“Isra’ila ba shi da ‘ya’ya ne?

Ko kuwa ba shi da māgada ne?

Me ya sa waɗanda suke bautar Milkom

suka mallaki inda Gad take zama,

Suka zauna a garuruwanta?

2 Domin haka lokaci yana zuwa,

Sa’ad da zan sa mutanen garin

Rabba ta Ammon su ji busar

yaƙi.

Rabba za ta zama kufai,

Za a ƙone ƙauyukanta da wuta,

Sa’an nan Isra’ila zai mallaki

waɗanda suka mallake shi.

Ni Ubangiji na faɗa.

3 “Ki yi kuka, ya Heshbon, gama Ai ta

zama kufai!

Ku yi kuka, ku mutanen Rabba, ku

sa tufafin makoki.

Ku yi gudu, kuna kai da kawowa a

cikin garuka,

Gama za a kai Milkom bauta tare da

firistocinsa da wakilansa.

4 Me ya sa kuke taƙama da

ƙarfinku,

Ƙarfinku da yake ƙarewa, ku mutane

marasa aminci?

Kun dogara ga dukiyarku,

Kuna cewa, ‘Wane ne zai iya gāba da

mu?’

5 Ga shi, zan kawo muku razana daga

waɗanda suke kewaye da ku,

Za a kore ku, kowane mutum zai

kama gabansa,

Ba wanda zai tattara ‘yan gudun

hijira.

Ni Ubangiji Allah Mai Runduna

na faɗa.

6 “Amma daga baya zan sa

Ammonawa su wadata kuma,

Ni Ubangiji na faɗa.”

Jawabin Ubangiji a kan Edom

7 Ga abin da Ubangiji Mai Runduna

ya faɗa a kan Edom,

“Ba hikima kuma a cikin Teman?

Shawara ta lalace a wurin masu

basira?

Hikima ta lalace ne?

8 Ku mazaunan Dedan, ku juya, ku

gudu,

Ku ɓuya cikin zurfafa,

Gama zan kawo masifa a kan Isuwa

A lokacin da zan hukunta shi,

9 Idan masu tsinkar ‘ya’yan inabi sun

zo wurinka

Ba za su rage abin kala ba?

Idan kuma ɓarayi sun zo da dare,

Za su ɗauki iyakacin abin da suke so

kurum.

10 Amma na tsiraita Isuwa sarai,

Na buɗe wuraren ɓuyarsa,

Har bai iya ɓoye kansa ba,

An hallakar da mutanen Isuwa

Tare da ‘yan’uwansa da

maƙwabtansa,

Ba wanda ya ragu.

11 Ka bar marayunka, ni zan rayar da

su.

Matanka da mazansu sun mutu,

Sai su dogara gare ni.”

12 Ubangiji ya ce, “Ga shi, waɗanda ba a shara’anta su ga shan ƙoƙon hukunci ba, za su sha shi, to, kai za ka kuɓuta? Ba za ka kuɓuta ba, amma lalle za ka sha shi!

13 Gama ni Ubangiji na rantse da zatina, cewa Bozara za ta zama abar tsoro, da abar dariya, da kufai, da abar la’ana. Dukan garuruwanta za su zama kufai har abada.”

14 Irmiya ya ce,

“Na karɓi saƙo daga wurin

Ubangiji.

An aiki jakada a cikin al’ummai

cewa,

‘Ku tattara kanku, ku zo ku yi gāba

da ita,

Ku tasar mata da yaƙi!’

15 Gama ga shi, zan maishe ki

ƙanƙanuwa cikin al’ummai,

Abar raini a wurin mutane.

16 Tsoronki da ake ji da girmankanki

sun ruɗe ki,

Ke da kike zaune a kogon dutse, a

kan tsauni,

Ko da yake kin yi gidanki can sama

kamar gaggafa,

Duk da haka zan komar da ke ƙasa,

Ni Ubangiji na faɗa.”

17 Ubangiji ya ce, “Edom za ta lalace, duk wanda ya bi ta wurin zai gigice, ya yi tsaki saboda dukan masifunta.

18 Abin da zai faru ga Edom zai zama daidai da abin da ya faru ga Saduma, da Gwamrata, da biranen da suke kusa da su, a lokacin da aka kaɓantar da su. Ba wanda zai zauna cikinta, ba wanda kuma zai yi zaman baƙunci a cikinta, ni Ubangiji na faɗa.

19 Kamar yadda zaki yakan fito daga cikin kurmin Urdun, garin ya fāda wa babban garken tumaki, haka zan sa nan da nan su gudu daga gare ta. Zan naɗa wani wanda na zaɓa, gama wa yake kama da ni? Wa zai yi ƙarata? Ina makiyayin da ya isa ya yi gāba da ni?

20 Domin haka, ku ji shirin da ni Ubangiji na yi wa Edom, da abin da nake nufin yi wa mazaunan Teman. Hakika za a tafi da su, har da ƙanana na garken tumaki, zan kuma sa wurin kiwonsu ya zama ƙeƙuwa saboda su.

21 Amon fāɗuwarsu zai sa ƙasa ta girgiza, za a kuma ji muryar kukansu har a Bahar Maliya.

22 Wani zai tashi da sauri, ya yi sama kamar gaggafa. Zai buɗe fikafikansa a kan Bozara. Zukatan sojojin Edom za su zama kamar zuciyar macen da take naƙuda.”

Jawabin Ubangiji a kan Dimashƙu

23 Ga abin da Ubangiji ya faɗa a kan Dimashƙu,

“Hamat da Arfad sun gigice,

Domin sun ji mugun labari,

sun narke saboda yawan damuwa,

Ba za su iya natsuwa ba.

24 Dimashƙu ta yi halin ƙaƙa naka yi,

Ta juya, ta gudu,

Tsoro ya kama ta,

Azaba da baƙin ciki sun kama ta

kamar na naƙuda.

25 Ƙaƙa aka manta da sanannen birni,

Birnin da take cike da murna?

26 A waccan rana samarinta za su fāɗi a

dandalinta.

Za a hallaka sojojinta duka,

Ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa.

27 Zan kuma sa wuta a garun Dimashƙu,

Za ta kuwa cinye fādodin

Ben-hadad.”

Jawabin Ubangiji a kan Kedar da Hazor

28 Ga abin da Ubangiji ya faɗa a kan Kedar da sarakunan Hazor, waɗanda sarki Nebukadnezzar ya ci da yaƙi,

“Ku tashi zuwa Kedar,

Ku hallaka mutanen gabas.

29 Za a kwashe alfarwansu da

garkunansu,

Da labulan alfarwansu, da dukan

kayansu.

Za a kuma tafi da raƙumansu,

Za a gaya musu cewa, ‘Razana ta

kewaye ku!’

30 “Ku mazaunan Hazor, ku gudu zuwa

nesa,

Ku ɓuya cikin zurfafa, ni Ubangiji na

faɗa,

Gama Nebukadnezzar, Sarkin

Babila, ya shirya muku

maƙarƙashiya,

Ya ƙulla mugun nufi game da ku.

31 Ku tashi ku fāɗa wa al’ummar da take

zama lami lafiya,

Waɗanda ba su da ƙofofi ko ƙyamare,

Suna zama su kaɗai.

32 “Za a washe raƙumansu da

garkunan shanunsu ganima,

Zan watsar da masu yin kwaskwas

ko’ina,

Zan kuma kawo musu masifu daga

kowace fuska,

Ni Ubangiji na faɗa.

33 Hazor za ta zama kufai har abada,

wurin zaman diloli,

Ba wanda zai zauna a ciki, ba wanda

kuma zai yi zaman baƙunci a wurin.”

Jawabin Ubangiji a kan Elam

34 Maganar da Ubangiji ya yi wa annabi Irmiya a kan Elam a farkon sarautar Zadakiya Sarkin Yahuza.

35 Ubangiji Mai Runduna ya ce,

“Zan karya bakan Elam, inda

ƙarfinta yake.

36 Zan sa iska ta hura a kan Elam daga

kusurwoyi huɗu na samaniya.

Za ta watsar da mutane ko’ina,

Har ba ƙasar da za a rasa mutumin

Elam a ciki.

37 Zan sa mutanen Elam su ji tsoron

maƙiyansu waɗanda suke neman

ransu.

Da zafin fushina zan kawo musu

masifa,

In sa a runtume su da takobi,

Har in ƙare su duka,

Ni Ubangiji na faɗa.

38 Zan kafa gadon sarautata a Elam,

Zan hallaka sarkinta da

shugabanninta.

39 Amma daga baya zan sa Elam kuma

ta wadata.

Ni Ubangiji na faɗa.”