IRM 48

Jawabin Ubangiji a kan Mowab

1 Ga abin da Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila ya faɗa a kan Mowab,

“Kaiton Nebo, gama ta lalace!

An kunyatar da Kiriyatayim, an ci ta

da yaƙi,

An kunyatar da kagararta, an rushe

ta.

2 Darajar Mowab ta ƙare.

Ana shirya mata maƙarƙashiya a

Heshbon,

‘Bari mu je mu ɓata ta daga zaman

al’umma!’

Ke kuma Madmen za ki yi shiru,

Takobi zai runtume ki.

3 Muryar kuka daga Horonayim tana

cewa,

‘Risɓewa da babbar halaka!’

4 “An hallakar da Mowab,

Ƙanananta suna kuka.

5 Gama a hawan Luhit, za su hau da

kuka,

Gama a gangaren Horonayim,

Suna jin kukan wahalar halaka.

6 Ku gudu don ku tserar da

rayukanku,

Ku gudu kamar jakin jeji.

7 “Kun dogara ga ƙarfinku da

wadatarku,

Amma yanzu za a ci ku da yaƙi,

Kemosh zai tafi bauta

Tare da firistocinsa da

shugabanninsa.

8 Mai hallakarwa zai shiga kowane

gari,

Don haka ba garin da zai tsira.

Kwari da tudu za su lalace,

Ni Ubangiji na faɗa.

9 Ku ba Mowab fikafikai,

Gama za ta tashi ta gudu,

Garuruwanta za su zama kango,

Ba mazauna cikinsu.

10 “La’ananne ne shi wanda yake yin

aikin Ubangiji da ha’inci,

La’ananne ne shi kuma wanda ya

hana wa takobinsa jini.

11 “Tun daga ƙuruciya Mowab tana

zama lami lafiya,

Hankali kwance,

Ba a jujjuya ta daga tulu zuwa tulu

ba,

Ba a taɓa kai ta bauta ba,

Domin haka daɗin ɗanɗanonta bai

rabu da ita ba,

Ƙanshinta kuma bai sāke ba.”

12 Ubangiji ya ce, “Domin haka kwanaki suna zuwa, sa’ad da zai aika da mutane su tuntsurar da tuluna, su zubar da ruwan inabi, su farfasa tulunanta.

13 Sa’an nan Kemosh zai kunyatar da Mowab, kamar yadda Betel wadda Isra’ilawa suka dogara gare ta ta kunyatar da su.

14 “Don me kake cewa,

‘Mu jarumawa ne, mayaƙan gaske?’

15 Mai hallaka Mowab da garuruwanta

ya taho,

Zaɓaɓɓun majiya ƙarfinta sun

gangara mayanka,

Ni sarki, mai suna Ubangiji Mai

Runduna, na faɗa.

16 Masifar Mowab ta kusato,

Halakarta kuma tana gaggabtowa.

17 “Ku yi makoki dominta, ku da kuke

kewaye da ita,

Dukanku da kuka san sunanta, ku

ce,

‘Ƙaƙa sandan sarauta mai iko

Da sanda mai daraja ya karye?’

18 Ku da kuke zaune a Dibon,

Ku sauka daga wurin zamanku mai

daraja,

Ku zauna a busasshiyar ƙasa,

Gama mai hallaka Mowab ya zo ya

yi gab da ku.

Ya riga ya rushe kagararku.

19 Ku mazaunan Arower,

Ku tsaya a kan hanya, ku jira,

Ku tambayi wanda yake gudu

Da wanda yake tserewa,

Abin da ya faru.

20 An kunyatar da Mowab, ta rushe.

Ku yi kuka dominta,

Ku faɗa a Arnon, cewa Mowab ta

halaka.

21 “Hukunci ya auka kan garuruwan da suke a ƙasar fili, wato Holon, da Yahaza, da Mefayat,

22 da Dibon, da Nebo, da Bet-diblatayim,

23 da Kiriyatayim, da Bet-gamal, da Ba’almeyon,

24 da Kiriyot, da Bozara. Hukunci ya zo a kan dukan garuruwan Mowab na nesa da na kusa.

25 An karye ikon Mowab da ƙarfinta, ni Ubangiji na faɗa.

26 “Ku sa Mowab ta yi maye domin ta tayar wa Ubangiji. Za ta yi birgima cikin amanta, mutane kuwa za su yi dariya.

27 Kin yi wa mutanen Isra’ila dariya. A kowane lokacin da kika ambaci sunansu, sai ki taɗa kanki da raini kamar an kama su tare da ɓarayi.

28 “Ku mazaunan Mowab, ku bar

garuruwanku,

Ku tafi, ku zauna a kogwanni,

Ku zama kamar kurciya wadda take

yin sheƙarta a bakin kwazazzabo.

29 Mun ji labarin girmankan Mowab,

da ɗaukaka kanta,

Da alfarmarta, da izgilinta,

Tana da girmankai ƙwarai.

30 Ni Ubangiji na san Mowab tana da

girmankai,

Alfarmarta ta banza ce,

Ayyukanta kuma na banza ne.

31 Don haka zan yi kuka saboda

Mowab duka,

Zan kuma yi baƙin ciki saboda

mutanen Kir-heres.

32 Zan yi kuka saboda kurangar inabin

Sibma

Fiye da yadda zan yi kuka saboda

mutanen Yazar.

Rassanku sun haye teku har sun kai

Yazar,

Amma mai hallakarwa ya faɗo a kan

‘ya’yan itatuwanku da damuna

Da kan amfanin inabinku.

33 An ɗauke farin ciki da murna daga

ƙasa mai albarka ta Mowab,

Na hana ruwan inabi malala daga

wurin matsewarsa,

Ba wanda yake matse shi, yana ihu na

murna,

Ihun da ake yi ba na murna ba ne.

34 “Mutanen Heshbon da na Eleyale suna kururuwa ana iya jin kururuwansu a Yahaza. Ana iya jinta kuma a Zowar, da Horonayim, da Eglat-shelishiya. Har ma ruwan Nimra ya ƙafe.

35 Zan hana mutanen Mowab miƙa hadayu na ƙonawa a tuddai, da miƙa wa gumakansu sadaka, ni Ubangiji na faɗa.

36 “Zuciyata tana makoki domin Mowab da Kir-heres kamar wanda yake kukan makoki da sarewa saboda wadatarsu ta ƙare.

37 Gama kowa ya aske kansa da gemunsa, sun tsattsage hannuwansu. Kowa kuma ya sa rigar makoki.

38 Ba abin da ake yi a bisa kan soraye da dandali na Mowab sai baƙin ciki, gama na farfashe Mowab kamar tulun da ba a so, ni Ubangiji na faɗa.

39 An farfashe Mowab, ta yi kuka, ta kunyata! Ta zama abin dariya da abin tsoro ga waɗanda suke kewaye da ita.

40 “Ni Ubangiji na ce,

Wani zai yi firiya da sauri kamar

gaggafa,

Zai shimfiɗa fikafikansa a kan

Mowab.

41 Za a ci garuruwa da kagarai da

yaƙi,

A wannan rana zukatan sojojin

Mowab

Za su zama kamar zuciyar macen da

take naƙuda.

42 Za a hallaka Mowab daga zaman

al’umma,

Domin ta tayar wa Ubangiji.

43 Tsoro, da rami, da tarko suna

jiranku,

Ya mazaunan Mowab,

Ni Ubangiji na faɗa.

44 Wanda ya guje wa tsoro,

Zai fāɗa a rami,

Wanda kuma ya fito daga cikin

rami,

Tarko zai kama shi.

Gama na sa wa Mowab lokacin da

zan hukunta ta,

Ni Ubangiji na faɗa.

45 “A ƙarƙashin inuwar Heshbon ‘yan

gudun hijira suna tsaye ba ƙarfi.

Gama wuta ta ɓullo daga Heshbon,

Harshen wuta kuma ya fito daga

Sihon,

Ta ƙone goshin Mowab da

ƙoƙwan kai na ‘yan tayarwa.

46 Kaitonku, ya Mowabawa!

Mutanen Kemosh sun lalace,

An kai ‘ya’yanku mata da maza

cikin bauta.

47 “Amma zan komar da mutanen

Mowab nan gaba,

Ni Ubangiji na faɗa.”

Wannan shi ne hukuncin Mowab.