ISH 61

Albishirin Ceto ga Sihiyona

1 Ubangiji ya saukar mini da ikonsa.

Ya zaɓe ni, ya aike ni

Domin in kawo albishir mai daɗi ga talakawa,

In warkar da waɗanda suka karai a zuci,

In yi shelar kwance ɗaurarru,

Da kuma ‘yanci ga waɗanda suke cikin kurkuku.

2 Ya aike ni in yi shela,

Cewa lokaci ya yi

Da Ubangiji zai ceci mutanensa,

Ya kuma ci nasara a kan abokan gābansu.

Ya aike ni domin in ta’azantar da masu makoki,

3 Domin in kawo wa masu makoki a Sihiyona

Farin ciki da murna maimakon baƙin ciki,

Waƙar yabo maimakon ɓacin rai.

Ubangiji kansa zai lura da su,

Za su ji daɗi kamar itace mai duhuwa.

Kowa da kowa zai aikata abin da yake daidai,

Za a yi yabon Allah saboda abin da ya yi.

4 Za su sāke gina biranen da suke a rurrushe tun da daɗewa.

5 Ya Urushalima, baƙi za su bauta miki,

Za su lura da garkunanki,

Za su nome gonakinki, su gyara gonakinki na inabi.

6 Amma za a sani, ku firistoci ne na Ubangiji,

Za ku mori dukiyar al’ummai,

Za ku yi fāriya da cewa, taku ce.

7 Kunyarku da shan wulakancinku za su ƙare.

Za ku zauna a ƙasarku,

Za a riɓanya dukiyarku,

Za ku yi ta farin ciki har abada.

8 Ubangiji ya ce,

“Ina ƙaunar aikin gaskiya,

Amma ina ƙin zalunci da aikata laifi.

Da aminci zan ba mutanena lada,

In yi madawwamin alkawari, da su.

9 Za su yi suna a cikin al’ummai,

Dukan wanda ya gan su zai sani,

Su ne mutanen da na sa wa albarka.”

10 Urushalima tana murna saboda abin da Ubangiji ya yi.

Tana kama da amaryar da ta sha ado a ranar aurenta.

Allah ya suturce ta da ceto da nasara.

11 Ba shakka, Ubangiji zai ceci jama’arsa,

Kamar yadda iri yakan tsiro ya yi girma.

Dukan al’ummai kuwa za su yi yabonsa.