LUK 2

Haihuwar Yesu

1 A kwanakin nan Kaisar Augustas ya yi shela, cewa a rubuta dukkan mutanen da suke ƙarƙashin mulkinsa.

2 Wannan shi ne ƙirga na fari da aka yi a zamanin Kiriniyas, mai mulkin ƙasar Suriya.

3 Kowa sai ya tafi garinsu a rubuta shi.

4 Yusufu shi ma ya tashi daga birnin Nazarat, a ƙasar Galili, ya tafi ƙasar Yahudiya, ya je birnin Dawuda, da ake kira Baitalami (domin shi daga gidan Dawuda ne, na cikin zuriyarsa),

5 don a rubuta shi, duk da Maryamu tashinsa, wadda take kuma da ciki.

6 Sa’ad da suke can kuwa, sai lokacin haihuwarta ya yi.

7 Sai ta haifi ɗanta na fari, ta rufi shi da zanen goyo, ta kuma kwantar da shi a wani komi dabbobi, don ba su sami ɗaki a masaukin ba.

Makiyaya da Mala’iku

8 A wannan yankin ƙasa kuwa waɗansu makiyaya suna kwana a filin Allah, suna tsaron garken tumakinsu da dad dare.

9 Sai ga wani mala’ikan Ubangiji tsaye kusa da su, ɗaukakar Ubangiji kuma ta haskaka kewayensu, har suka tsorata gaya,

10 Sai mala’ikan ya ce musu, “Kada ku ji tsoro, ga shi, albishir na kawo muku na farin ciki mai yawa, wanda zai zama na dukan mutane.

11 Domin yau an haifa muku Mai Ceto a birnin Dawuda, wanda yake shi ne Almasihu, Ubangiji.

12 Ga alamar da za ku gani, za ku sami jariri rufe da zanen goyo, kwance a komin dabbobi.”

13 Ba labari sai ga taron rundunar Sama tare da mala’ikan nan, suna yabon Allah, suna cewa,

14 “Ɗaukaka ga Allah ta tabbata, can cikin Sama mafi ɗaukaka.

A duniya salama ta tabbata, ga mutanen da yake murna da su matuƙa.”

15 Da mala’iku suka tafi daga gare su suka koma Sama, sai makiyayan suka ce wa juna, “Mu tafi Baitalami yanzu, mu ga abin nan da ya faru, wanda Ubangiji ya sanar da mu.”

16 Sai suka tafi da hanzari, suka sami Maryamu da Yusufu, da kuma jaririn kwance a komin dabbobi.

17 Da suka gan shi, suka bayyana maganar da aka faɗa musu game da wannan ɗan yaro.

18 Duk waɗanda suka ji kuma, suka yi ta al’ajabin abin da makiyayan nan suka faɗa musu.

19 Maryamu kuwa sai ta riƙe duk abubuwan da aka faɗa, tana biya su a zuci.

20 Makiyayan suka koma, suna ta ɗaukaka Allah, suna yabonsa, saboda duk abin da suka ji, suka kuma gani, yadda aka gaya musu.

Kaciyar Yesu

21 Da rana ta takwas ta kewayo da za a yi masa kaciya, aka sa masa suna Yesu, wato sunan da mala’ika ya faɗa kafin ya zauna a ciki.

Miƙa Yesu a Haikali

22 Da kwanakin tsarkakewarsu suka cika bisa ga Shari’ar Musa, suka kawo shi Urushalima, su miƙa shi ga Ubangiji

23 (kamar dai yadda yake a rubuce a Shari’ar Ubangiji cewa, “Duk ɗan farin da aka haifa, za a ce da shi tsattsarka ne Ubangiji”),

24 su kuma yi hadaya bisa ga abin da aka faɗa a Shari’ar Ubangiji cewa, “Kurciyoyi biyu, ko kuwa ‘yan shila biyu.”

25 To, akwai wani mutum a Urushalima, mai suna Saminu, adali, mai bautar Allah, yana kuma ɗokin ganin ta’aziyyar Isra’ila. Ruhu Mai Tsarki kuwa yana tare da shi.

26 Ruhu Mai Tsarki kuwa ya riga ya bayyana masa, cewa ba zai mutu ba sai ya ga Almasihun Ubangiji.

27 Ruhu na iza shi, sai ya shiga Haikalin. Da iyayen suka shigo da ɗan yaron nan Yesu, su yi masa yadda ka’idar Shari’ar ta ce,

28 sai Saminu ya rungume shi, ya yi wa Allah godiya, ya ce,

29 “Yanzu kam, ya Mamallaki,

Sai ka sallami bawanka lafiya,

Bisa ga abin da ka faɗa,

30 Don na ga cetonka zahiri,

31 Da ka shirya a gaban kabilai duka,

32 Haske mai bayyana wa alummai hanyarka,

Da kuma ɗaukakar jama’arka Isra’ila.”

33 Uwa tasa da ubansa kuwa suna mamakin abin da aka faɗa game da shi,

34 Sai Saminu ya sa musu albarka, ya ce wa Maryamu uwar Yesu,

“Kin ga wannan yaro, shi aka sa ya zama sanadin faɗuwar waɗansu, tashin waɗansu kuma da yawa cikin Isra’ila,

Zai kuma zama alama wadda ake kushenta,

35 Domin tunanin zukata da yawa su bayyana.

I, ke ma, takobi zai tsaga zuciyarki.”

36 Akwai kuma wata annabiya, mai suna Hannatu, ‘yar Fanuyila, na kabilar Ashiru. Ta kuwa tsufa ƙwarai, ta yi zaman aure shekara bakwai bayan ɗaukanta na budurci,

37 da mijinta ya mutu kuma ta yi zaman gwauranci har shekara tamanin da huɗu. Ba ta rabuwa da Haikalin, tana bauta wa Allah dare da rana ta wurin yin addu’a da azumi.

38 Nan take ita ma ta zo, ta yi wa Allah godiya, ta kuma yi maganar ɗan yaron nan ga dukan masu sauraron fansar Urushalima.

Komawa Nazarat

39 Bayan sun ƙare kome da kome bisa ga Shari’ar Ubangiji, sai suka koma ƙasar Galili suka tafi garinsu Nazarat.

40 Ɗan yaron kuwa ya girma, ya kawo ƙarfi, yana mai matuƙar hikima. Alherin Allah kuwa yana tare da shi.

Yesu, Ɗan Saurayi, ya Shiga Haikali

41 To, iyayensa sukan je Urushalima kowace shekara a lokacin Idin Ƙetarewa.

42 Da ya shekara goma sha biyu, sai suka tafi tare da shi bisa ga al’adarsu a lokacin Idi.

43 Da aka gama idin kuma, suna cikin komowa, sai yaron, wato Yesu, ya tsaya a Urushalima, ba da sanin iyayensa ba.

44 Su kuwa suka yi ta tafiya yini guda, suna zaton yana cikin ayari. Sai suka yi ta cigiyarsa cikin ‘yan’uwansu da idon sani.

45 Da ba su same shi ba, suka koma Urushalima, suna ta cigiyarsa.

46 Sai kuma a rana uku suka same shi a Haikalin zaune a tsakiyar malamai, yana sauraronsu, yana kuma yi musu tambayoyi.

47 Duk waɗanda suka ji shi kuwa suka yi al’ajabin irin fahimtarsa da amsoshinsa.

48 Da suka gan shi suka yi mamaki, sai uwa tasa ta ce masa, “Ya kai ɗana, yaya ka yi mana haka? Ga shi nan, ni da babanka muna ta nemanka duk ranmu a ɓace.”

49 Sai ya ce musu, “Me ya sa kuka yi ta nemana? Ashe, ba ku sani wajibi ne in yi sha’anin Ubana ba?”

50 Amma ba su fahimci maganar da ya yi musu ba.

51 Sai ya koma Nazarat tare da su, yana yi musu biyayya. Uwa tasa kuwa na riƙe da dukan abubuwan nan a ranta.

52 Yesu kuwa ya yi ta ƙaruwa da hikima, da girma, da kuma tagomashi wurin Allah da mutane.