MIKA 1

1 Ubangiji ya yi magana da Mika mutumin Moreshet a zamanin Yotam, da na Ahaz, da na Hezekiya, sarakunan Yahuza. Ya yi masa magana a kan Samariya da Urushalima.

Makoki don Samariya da Urushalima

2 Dukanku ku ji, ku al’ummai!

Ki kasa kunne, ya duniya, da dukan

abin da yake cikinki.

Bari Ubangiji Allah

Daga Haikalinsa mai tsarki ya zama

shaida a kanku.

3 Ga shi, Ubangiji yana fitowa daga

wurin zamansa,

Zai sauko, ya taka kan tsawawan

duwatsun duniya.

4 Duwatsu za su narke a

ƙarƙashinsa,

Kwaruruka za su tsattsage kamar

kakin zuma a gaban wuta,

Kamar ruwa yana gangarowa daga

tsauni.

5 Duk wannan kuwa saboda laifin

Yakubu ne,

Da laifin Isra’ila.

Mene ne laifin Yakubu?

Ashe, ba bautar gumaka da zaluncin

da ake yi a Samariya ba?

Mene ne kuma laifin Yahuza?

Ashe, ba bautar gumaka da zaluncin

da ake yi a Urushalima ba?

6 “Domin haka zan mai da Samariya

jujin kufai a karkara,

Wurin dasa kurangar inabi.

Zan zubar da duwatsunta a cikin

kwari,

In tone harsashin gininta.

7 Za a farfashe dukan siffofinta na

zubi,

Za a ƙaƙƙone dukiyarta da wuta,

Zan lalatar da gumakanta duka,

Gama ta wurin karuwanci ta samo

su,

Ga karuwanci kuma za su koma.”

8 Mika ya ce, “Saboda wannan zan yi

baƙin ciki, in yi kuka,

Zan tuɓe, in yi tafiya huntu.

Zan yi kuka kamar diloli,

In yi baƙin ciki kamar jiminai.

9 Gama raunin Samariya, ba ya

warkuwa,

Gama ya kai Yahuza,

Ya kuma kai ƙofar jama’ata a

Urushalima.”

10 Kada a faɗe shi a Gat,

Sam, kada a yi kuka.

Yi birgima cikin ƙura a Bet-leyafra.

11 Ku mazaunan Shafir, ku wuce

abinku da tsiraici da kunya.

Mazaunan Za’anan ba su tsira ba.

Bet-ezel ta yi kururuwa, “Zai

tumɓuke harasashin gininki.”

12 Mutanen Marot sun ƙosa su ga

alheri,

Amma masifa ta zo ƙofar

Urushalima daga wurin Ubangiji.

13 Ku mutanen Lakish, ku ɗaura wa

dawakai karusai,

Gama ku kuka fara yin zunubi a

Sihiyona,

Gama an iske laifofin Isra’ila

cikinku.

14 Domin haka sai ku ba Moreshet-gat

guzuri,

Mutanen Akzib za su yaudari

sarakunan Isra’ila.

15 Ku mazaunan Maresha, Ubangiji zai

kawo wanda zai ci ku da yaƙi,

Darajar Isra’ila za ta shiga

Adullam.

16 Ku aske kanku saboda ƙaunatattun

‘ya’yanku.

Ku yi wa kanku ƙwaƙwal kamar

ungulu,

Gama ‘ya’yanku za su tafi bautar

talala.