MIKA 2

Taku ta Ƙare, Ku Masu Zaluntar Matalauta

1 Taku ta ƙare, ku masu shirya

mugunta,

Masu tsara mugunta a gadajensu!

Sa’ad da gari ya waye, sai su aikata

ta,

Domin ikon aikatawa yana

hannunsu.

2 Sukan yi ƙyashin gonaki da gidaje,

sai su ƙwace.

Sukan zalunci mutum, su ƙwace

gidansa da gādonsa.

3 Domin haka Ubangiji ya ce,

Ga shi, yana shirya wa wannan

jama’a masifa,

Wadda ba za ku iya kuɓuta daga

cikinta ba.

Ba kuma za ku yi tafiyar alfarma ba,

Gama mugun lokaci ne.

4 A wannan rana za su yi karin

magana a kanku,

Za su yi kuka da baƙin ciki mai

zafi,

Su ce, “An lalatar da mu sarai!

Ya sāke rabon mutanena,

Ya kawar da shi daga gare ni!

Ya ba da gonakinmu ga waɗanda

suka ci mu da yaƙi.”

5 Don haka ba za ku sami wanda zai sa

muku ma’auni

A taron jama’ar Ubangiji ba.

6 “Kada su yi wa’azi,” amma sun yi

wa’azi.

“Idan ba su yi wa’azi a kan

abubuwan nan ba,

Raini ba zai ƙare ba.

7 Daidai ne a faɗi haka, ya jama’ar

Yakubu?

‘Ruhun Ubangiji ya yi rashin haƙuri

ne?

Waɗannan ayyukansa ne?’ ”

“Ashe, maganata ba takan amfana

wanda yake tafiya daidai ba?”

8 Ubangiji ya amsa ya ce,

“Ba da daɗewa ba mutanena sun

tashi kamar maƙiyi,

Kukan tuɓe rigar masu wucewa da

salama, masu komawa da yaƙi.

9 Kukan kori matan mutanena

Daga gidajensu masu kyau,

Kukan kawar da darajata har abada

daga wurin ‘ya’yansu.

10 Ku tashi, ku tafi,

Gama nan ba wurin hutawa ba ne,

Saboda ƙazantarku wadda take kawo

muguwar hallaka.

11 “Idan mutum ya tashi yana iskanci,

yana faɗar ƙarya, ya ce,

‘Zan yi muku wa’azi game da ruwan

inabi da abin sa maye,’

To, shi ne zai zama mai wa’azin

mutanen nan!

12 “Hakika zan tattara ku duka, ya

Yakubu,

Zan tattara ringin Isra’ila.

Zan haɗa su tare kamar tumaki a

garke,

Kamar garken tumaki a makiyaya

Za su zama taron jama’a mai

hayaniya.

13 “Wanda zai huda garu, shi zai yi musu

jagora,

Za su fita ƙofar, su wuce, su fice ta

cikinta.

Sarkinsu zai wuce gabansu,

Ubangiji kuma yana kan gaba.”