MIKA 5

1 Ki tattara sojojinki, gama an

kewaye mu da yaƙi.

Za su bugi kumatun Sarkin Isra’ila

da sanda.”

Mulkin Mai Ceto daga Baitalami

2 “Baitalami cikin Efrata,

Wadda kike ‘yar ƙarama a cikin

kabilar Yahuza,

Amma daga cikinki wani zai fito

wanda zai sarauci Isra’ila

Wanda asalinsa tun fil azal ne.”

3 Domin haka zai yashe su,

Sai lokacin da wadda take naƙuda ta

haihu.

Sa’an nan sauran ‘yan’uwansa

Za su komo wurin mutanen Isra’ila.

4 Shi kuwa zai tashi ya ciyar da

garkensa da ƙarfin Ubangiji,

Da ɗaukakar sunan Ubangiji

Allahnsa.

Za su kuwa zauna lafiya,

Gama zai zama mai girma cikin

duniya duka.

5 Zai zama salamarmu.

Ceto da Hukunci

Sa’ad da kuma Assuriyawa za su

kawo mana yaƙi,

Za su tattake kagaranmu,

Za mu sa makiyaya bakwai da

shugabanni takwas su yi gāba da

su.

6 Za su mallaki ƙasar Assuriya da

takobi,

Su shiga ƙofofin ƙasar Nimrod da

zararren takobi,

Zai cece mu daga hannun

Ba’assuriye,

Sa’ad da ya kawo wa ƙasarmu

yaƙi,

Sa’ad da kuma ya tattake ƙasarmu.

7 Sa’an nan ringin Yakubu zai zamar

wa mutane

Kamar raɓa daga wurin Ubangiji,

Kamar kuma yayyafi a kan tsire-

tsire,

Wanda ba ya jinkiri ko ya jira

mutane.

8 Ringin Yakubu kuma zai zamar wa

al’umman duniya,

Kamar yadda zaki yake a tsakanin

namomin jeji,

Kamar kuma yadda zaki yake a

tsakanin garkunan tumaki,

Wanda, sa’ad da ya ratsa, yakan

tattaka,

Ya yi kacakaca da su,

Ba wanda zai cece su.

9 Za a ƙarfafa hannunka a kan

maƙiyanka,

Za a datse maƙiyanka duka.

10 “A wannan rana, ni Ubangiji na ce,

Zan kashe dawakanku, in hallaka

karusanku.

11 Zan shafe biranen ƙasarku,

In rushe garunku.

12 Zan kawar da maita daga ƙasarku,

Ba za ku ƙara samun bokaye ba.

13 Zan sassare siffofinku da

ginshiƙanku,

Ba za ku ƙara sunkuya wa aikin

hannuwanku ba.

14 Zan tumɓuke gumakan nan Ashtarot

daga cikinku,

Zan hallaka biranenku.

15 Da fushi da hasala zan yi sakayya

A kan al’umman da ba su yi biyayya

ba.”