MIKA 4

Mulkin Salama na Ubangiji

1 Zai zama nan gaba, dutse inda

Haikalin Ubangiji yake

Zai zama shi ne mafi tsawo duka a

cikin duwatsu,

Zai fi tuddai tsayi,

Mutane kuwa za su riƙa ɗunguma

zuwa wurinsa.

2 Al’umman duniya za su zo, su ce,

“Bari mu haura zuwa tudun

Ubangiji,

Zuwa Haikalin Allah na Isra’ila,

Za mu koyi abin da yake so mu yi,

Za mu yi tafiya a hanyar da ya

zaɓa.”

Koyarwar Ubangiji daga Urushalima

take zuwa,

Daga Sihiyona yake magana da

jama’arsa.

3 Zai shara’anta tsakanin al’umman

duniya masu yawa,

Zai sulhunta jayayyar da take tsakanin

manyan al’ummai,

Za su mai da takubansu garemani,

Māsunsu kuma su maishe su

wuƙaƙen aske itace.

Al’umma ba za ta ƙara fita zuwa

yaƙi ba,

Ba za su ƙara koyon yaƙi ba.

4 Kowa zai zauna gindin kurangar

inabinsa da gindin ɓaurensa.

Ba wanda zai tsoratar da shi,

Gama Ubangiji Mai Runduna ne ya

faɗa.

5 Ko da yake al’ummai suna bin

gumakansu,

Amma mu za mu bi Ubangiji

Allahnmu har abada abadin.

Kuɓutar Isra’ila daga Zaman Talala

6 Ubangiji ya ce,

“A waccan rana zan tattara guragu,

Da waɗanda aka kora,

Da waɗanda na wahalshe su.

7 Zan sa guragu su wanzu,

Korarru kuwa su zama al’umma mai

ƙarfi,

Ni, Ubangiji, zan yi mulkinsu a

Sihiyona har abada.

8 “Ke kuma hasumiyar garken tumaki,

tudun Sihiyona,

Mulki na dā zai komo wurinki,

Wato sarautar Urushalima.”

9 Yanzu, me ya sa kike kuka da

ƙarfi?

Ba sarki a cikinki ne?

Mashawarcinki ya hallaka ne,

Da azaba ta auka miki kamar ta

mace mai naƙuda?

10 Ki yi makyarkyata, ki yi nishi, ke

Sihiyona,

Kamar mace mai naƙuda,

Gama yanzu za ki fita daga cikin

birni,

Ki zauna a karkara,

Za ki tafi Babila, daga can za a cece

ki.

Daga can Ubangiji zai cece ki daga

hannun maƙiyanki.

11 Yanzu al’ummai sun taru suna

gāba da ke, suna cewa,

“Bari a ƙazantar da ita,

Bari mu zura mata ido.”

12 Amma ba su san nufin Ubangiji ba,

Ba su gane shirinsa ba,

Gama ya tara su ne kamar

dammunan da za a kai

masussuka.

13 “Ya Sihiyona, ki tashi, ki tattaka!

Gama zan mai da ƙahonki ƙarfe,

kofatanki kuwa tagulla,

Za ki ragargaje al’ummai da yawa.”

Za ki ba Ubangijin dukan duniya

dukiyarsu da suka tara ta hanyar

zamba,

Wadatarsu kuma ga Ubangijin dukan

duniya.