NAH 3

1 Kaiton birnin jini,

Wanda yake cike da ƙarairayi da

ganima,

Da waso kuma ba iyaka!

2 Ku ji amon bulala da kwaramniyar

ƙafafu,

Da sukuwar doki da girgizar karusai!

3 Sojojin dawakai suna kai sura,

Takuba suna walƙiya, māsu suna

ƙyalƙyali.

Ga ɗumbun kisassu, da tsibin

gawawwaki,

Matattu ba su ƙidayuwa,

Suna tuntuɓe a kan gawawwaki!

4 Ya faru saboda yawan karuwancin

Nineba kyakkyawa mai daɗin

baki,

Wadda ta ɓad da al’umman duniya

da karuwancinta,

Ta kuma ɓad da mutane da daɗin

bakinta.

5 Ubangiji Mai Runduna ya ce, “Ina

gāba da ke,

Zan kware fatarinki a idonki,

Zan sa al’ummai da mulkoki su dubi

tsiraicinki.

6 Zan watsa miki ƙazanta,

In yi miki wulakanci,

In maishe ki abin raini.

7 Dukan waɗanda za su dube ki

Za su ja da baya su ce,

‘Nineba ta lalace, wa zai yi kuka

dominta?’

A ina zan samo miki waɗanda za su

ta’azantar da ke?”

8 Kin fi No ne?

Wadda take a bakin Nilu,

Wadda ruwa ya kewaye ta?

Teku ce kagararta.

Ruwa ne kuma garunta.

9 Habasha da Masar su ne ƙarfinta

marar iyaka,

Fut da Libiya su ne kuma

mataimakanta.

10 Duk da haka an tafi da ita, an kai ta

cikin bauta.

An fyaɗa ƙanananta a ƙasa,

An yi kacakaca da su a kowace

mararraba.

An jefa kuri’a a kan manyan

mutanenta,

Aka ɗaure dukan manyan mutanenta

da sarƙoƙi.

11 Ke Nineba kuma za ki bugu,

Za a ɓoye ki.

Za ki nemi mafaka a wurin maƙiyinki.

12 Dukan kagaranki suna kama da

itatuwan ɓaure,

Waɗanda ‘ya’yansu suka harba.

Da an girgiza sai su faɗo a bakin mai

sha.

13 Sojojinki kamar mata suke a

tsakiyarki!

An buɗe wa maƙiyanki ƙofofin

ƙasarki.

Wuta za ta cinye madogaran

ƙofofinki.

14 Ki tanada ruwa domin za a kewaye

ki da yaƙi!

Ki ƙara ƙarfin kagaranki!

Ki tafi kududdufi, ki kwaɓa laka!

Ki ɗauki abin yin tubali!

15 A can wuta za ta cinye ki,

Takobi zai sare ki,

Zai cinye ki kamar fara.

Ki riɓaɓɓanya kamar fara.

Ki kuma riɓaɓɓanya kamar ɗango.

16 Kin yawaita ‘yan kasuwanki suna da

yawa fiye da taurari,

Amma sun tafi kamar fara waɗanda

sukan buɗe fikafikansu su tashi, su

tafi.

17 Shugabanninki kamar ɗango suke,

Manyan mutanenki kamar

cincirindon fāra ne,

Suna zaune a kan shinge a kwanakin

sanyi,

Sa’ad da rana ta fito, sukan tashi su

tafi,

Ba wanda ya san inda suke.

18 Ya Sarkin Assuriya, masu tsaronka

suna barci,

Manyan mutanenka suna

kwankwance,

Mutanenka sun watse cikin

duwatsu,

Ba wanda zai tattaro su.

19 Ba abin da zai rage zafin rauninka,

Rauninka ba ya warkuwa.

Duk wanda ya ji labarinka, zai tafa

hannuwansa

Gama wane ne ba ka musguna wa

ba?