OBA 1

Ƙasƙancin Edom

1 Annabcin Obadiya ke nan.

Wannan shi ne abin da Ubangiji Allah ya ce a kan al’ummar Edom.

Ubangiji ya aiki manzonsa wurin

sauran al’umma,

Mun kuwa ji saƙonsa cewa,

“Ku zo! Mu tafi mu yi yaƙi da

Edom!”

2 Ubangiji ya ce wa al’ummar Edom,

“Zan maishe ki ƙanƙanuwa a cikin

sauran al’umma,

Za a raina ki ƙwarai.

3 Girmankanki ya yaudare ki,

Kina zaune a kagara, a kan dutse,

Wurin zamanki yana can

ƙwanƙolin duwatsu.

Don haka a zuciya kike cewa,

‘Wa zai saukar da ni ƙasa?’

4 Ko da yake kina shawagi can sama

kamar gaggafa,

Gidanki kuma yana can cikin taurari,

Daga can zan saukar da ke,” in ji

Ubangiji

5 “Idan ɓarayi sun shiga gidanki,

Idan kuma ‘yan fashi sun shiga

gidanki da dare,

Yaya za su washe ki?

Za su sace abin da ya ishe su ne

kaɗai,

Idan kuma ɓarayin ‘ya’yan inabi

sun shiga gonar inabinki,

Za su bar miki kala kurum.

6 Isuwa, wato Edom, ga taskarka,

An washe ta ƙaƙaf!

7 Waɗanda kake amana da su,

Za su kore ka daga ƙasarka.

Mutanen da suke amana da kai,

Za su yaudare ka,

Su ci ka da yaƙi.

Abokan nan naka da kake ci tare da

su za su kafa maka tarko,

Sa’an nan su ce, ‘Ina dukan wayon

nan nasa?’ ”

8 Ni Ubangiji na ce, “A ranar da zan

hukunta Edom,

Zan hallaka masu hikimarka,

Zan shafe hikima daga dutsen

Isuwa.

9 Jarumawanka za su firgita, ya

Teman,

Za a kashe kowane mutum daga

dutsen Isuwa.

10 “Saboda kama-karyar da ka yi wa

Yakubu ɗan’uwanka,

Za a sa ka ka sha kunya,

Za a hallaka ka har abada.

11 A ranan nan ka tsaya kawai,

A ranar da abokan gāba suka fasa

ƙofofinsa.

Suka kwashe dukiyarsa,

Suka jefa kuri’a a kan Urushalima.

Ka zama kamar ɗaya daga cikinsu.

12 Ba daidai ba ne ka yi murna

Saboda wahalar da ta sami

ɗan’uwanka.

Ba daidai ba ne ka yi farin ciki

Saboda halakar mutanen Yahuza.

Ba daidai ba ne ka yi musu dariya

A ranar wahalarsu.

13 Ba daidai ba ne ka shiga ƙofar

jama’ata

A ranar da suke shan masifa.

Ba daidai ba ne ka yi murna

A kan bala’in ɗan’uwanka.

Ba daidai ba ne ka washe dukiyarsa

A ranar masifarsa.

14 Ba daidai ba ne ka tsaya a mararraba,

Don ka kashe waɗanda suke ƙoƙarin

tserewa.

Ba daidai ba ne ka ba da waɗanda

suka tsere a hannun maƙiyansu

A ranar wahala.”

Hukuncin Al’ummai

15 “Ranar da ni Ubangiji zan

shara’anta al’ummai duka ta zo

kusa,

Ke, Edom, abin da kika yi,

Shi ne za a yi miki.

Ayyukanki za su koma a kanki.

16 Kamar yadda kuka sha hukunci a

kan tsattsarkan dutsena,

Haka dukan sauran al’umma za su yi

ta sha.

Za su sha, su yi tangaɗi,

Su zama kamar ba su taɓa kasancewa

ba.”

Cin Nasarar Isra’ila

17 “Amma za a sami waɗanda za su

tsira daga Dutsen Sihiyona,

Dutsen zai zama wuri ne mai tsarki.

Jama’ar Yakubu za ta mallaki

mallakarta.

18 Jama’ar Yakubu za ta zama kamar

wuta,

Jama’ar Yusufu kuwa kamar

harshen wuta,

Jama’ar Isuwa za ta zama kamar

tattaka.

Za su ƙone ta, su ci ta, ba wanda zai

tsira.

Ni Ubangiji na faɗa.”

19 Isra’ilawan da yake Negeb za su

mallaki dutsen Isuwa,

Waɗanda suke a filaye na Yahuza za su

mallaki ƙasar Filistiya.

Isra’ilawa za su mallaki yankin

ƙasar Ifraimu da Samariya,

Jama’ar Biliyaminu za su mallaki

Gileyad.

20 Rundunar masu zaman talala na

Isra’ilawa

Za su mallaki Kan’aniyawa har zuwa

Zarefat.

Masu zaman talala na Urushalima da

suke a Sefarad

Za su mallaki biranen Negeb.

21 Isra’ilawa za su hau Dutsen

Sihiyona, su cece shi,

Za su mallaki dutsen Isuwa,

Ubangiji ne Sarki.