YAH 7

‘Yan’uwan Yesu Ba Su Gaskata da Shi Ba

1 Bayan haka, Yesu ya riƙa zagawa a Ƙasar Galili, bai yarda ya zaga ta Yahudiya ba, don Yahudawa suna neman kashe shi.

2 Idin Bukkoki na Yahudawa kuwa ya gabato.

3 Sai ‘yan’uwansa suka ce masa, “Tashi daga nan mana ka tafi ƙasar Yahudiya, almajiranka su ma su ga ayyukan da kake yi.

4 Ai, ba mai aiki a ɓoye in yana so ya shahara. Tun da yake kana yin waɗannan al’amura, to, sai ka bayyana kanka ga duniya.”

5 Domin ko dā ma ‘yan’uwansa ba su gaskata da shi ba.

6 Sai Yesu ya ce musu, “Lokacina bai yi ba tukuna, amma ku, koyaushe lokacinku ne.

7 Ba dama duniya ta ƙi ku, amma ni take ƙi, don na shaide ta a kan ayyukanta mugaye ne.

8 Ku dai ku tafi idin. Ni ba za ni ba yanzu, don lokacina bai yi sosai ba tukuna.”

9 Da ya faɗa musu haka, ya dakata a ƙasar Galili.

Yesu a Idin Bukkoki

10 Bayan ‘yan’uwansa sun tafi idin kuwa, shi ma ya tafi, amma a ɓoye, ba a fili ba.

11 Yahudawa suna ta nemansa a wurin idin suna cewa, “Ina yake ne?”

12 Taro kuma suka riƙa maganarsa a raɗe, waɗansu na cewa, “Mutum ne nagari.” Waɗansu kuma na cewa, “A’a, ai, ɓad da jama’a yake.”

13 Amma ba wanda ya yi magana tasa a fili don tsoron Yahudawa.

14 Wajen tsakiyar idin sai Yesu ya shiga Haikali ya koyar.

15 Yahudawa suka yi mamakin abin, suka ce, “Yaya mutumin nan yake da karatu haka, ga shi kuwa, bai taɓa koyo ba?”

16 Sai Yesu ya amsa musu ya ce, “Koyarwata ba tawa ba ce, ta wanda ya aiko ni ce.

17 Duk mai son aikata nufin Allah zai san koyarwan nan ko ta Allah ce, ko domin kaina nake faɗa.

18 Mai magana don kansa, neman ɗaukakar kansa yake yi. Amma mai neman ɗaukakar wanda ya aiko shi, shi ne mai gaskiya, ba kuwa rashin gaskiya a gare shi.

19 Ashe, ba Musa ne ya ba ku Shari’a ba? Duk da haka ba mai kiyaye Shari’ar a cikinku. Don me kuke neman kashe ni?”

20 Taron suka amsa suka ce, “Kana da iska! Wa yake neman kashe ka?”

21 Yesu ya amsa musu ya ce, “Aiki ɗaya kawai na yi, dukanku kuwa kuna mamakinsa.

22 Musa ya bar muku kaciya, (ba ko shi ya fara ba, tun kakannin kakanni ne), ga shi kuma, kukan yi wa mutum kaciya ko a ran Asabar ma.

23 To, in ana yi wa mutum kaciya ran Asabar don gudun keta Shari’ar Musa, kwa yi fushi don na warkar da mutum sarai ran Asabar?

24 Kada ku yi hukunci da zato, amma ku yi hukunci da adalci.”

Wannan Almasihu Ne?

25 Sai waɗansu mutanen Urushalima suka ce, “Ashe, ba wannan ne mutumin da suke nema su kashe ba?

26 Ga shi nan kuwa, yana magana a fili, ba su ce masa kome ba! Ya yiwu kuma shugabanni sun san lalle wannan shi ne Almasihu?

27 Wannan kam, mun san daga inda yake, amma sa’ad da Almasihu ya zo ba wanda zai san daga inda yake.”

28 Yesu yana koyarwa a Haikalin ke nan, sai ya ɗaga murya ya ce, “Kun dai san ni, kun kuma san daga inda nake. Ban fa zo domin kaina ba. Wanda ya aiko ni mai gaskiya ne, shi kuwa ba ku san shi ba.

29 Ni na san shi, domin daga wurinsa na fito, shi ne kuwa ya aiko ni.”

30 Don haka suka nema su kama shi, amma ba wanda ya taɓa shi, domin lokacinsa bai yi ba tukuna.

31 Duk da haka mutane da yawa cikin taron sun gaskata da shi, suna cewa, “Sa’ad da Almasihu ya zo, zai yi mu’ujizai fiye da na mutumin nan?”

An Aiki Dogaran Haikalin Su Kamo Yesu

32 Farisiyawa suka ji taro suna raɗeraɗinsa haka, sai manyan firistoci da Farisiyawa suka aiki dogaran Haikali su kamo shi.

33 Sai Yesu ya ce, “Saurana ɗan lokaci kaɗan tare da ku, sa’an nan zan koma wurin wanda ya aiko ni.

34 Za ku neme ni, amma ba za ku same ni ba. Inda nake kuwa ba za ku iya zuwa ba.”

35 Sai Yahudawa suka ce wa juna, “Ina za shi da har ba za mu same shi ba? Za shi wurin Yahudawan da suka warwatsu a cikin al’ummai ne, ya koya wa al’umman?

36 Me kuma yake nufi da cewa, ‘Za ku neme ni amma ba za ku same ni ba’? da kuma cewa, ‘Inda nake ba za ku iya zuwa ba’?”

Kogunan Ruwan Rai

37 A ranar ƙarshe ta idin, wato babbar ranar, sai Yesu ya tsaya, ya ɗaga murya ya ce, “Duk mai jin ƙishirwa yă zo gare ni yă sha.

38 Duk mai gaskatawa da ni, kamar yadda Nassi ya ce, ‘Daga zuciyarsa ne kogunan ruwan rai za su gudana.’ ”

39 To, wannan shi ne ya faɗa game da Ruhu, wanda masu gaskatawa da shi za su karɓa, domin har yanzu ba a ba da Ruhu ba, saboda ba a ɗaukaka Yesu ba tukuna.

Rabuwa ta Shiga Tsakanin Mutane

40 Da jin maganan nan waɗansu daga cikin taron suka ce, “Hakika wannan annabin nan ne.”

41 Waɗansu kuwa suka ce, “Wannan Almasihu ne.” Amma waɗansu suka ce, “Me? Ashe, Almasihu daga ƙasar Galili zai fito?

42 Nassi ba cewa ya yi Almasihu zuriyar Dawuda ne ba, daga kuma Baitalami yake, ƙauyen da Dawuda ya zauna?”

43 Sai kuma rabuwa ta shiga tsakaninsu a kansa.

44 Waɗansunsu suka so su kama shi, amma ba wanda ya taɓa shi.

Shugabanni Ba Su Gaskata da Yesu Ba

45 Daga nan dogaran Haikali suka koma wurin manyan firistoci da Farisiyawa, su kuwa suka ce musu, “Don me ba ku kawo shi ba?”

46 Sai dogaran suka amsa suka ce, “A’a, ba mutumin da ya taɓa magana kamar wannan!”

47 Sai Farisiyawa suka amsa musu suka ce, “Af! Har ku ma an ɓad da ku ne?

48 Ashe, akwai wani daga cikin shugabanni ko Farisiyawa da ya gaskata da shi?

49 Amma wannan taro da ba su san Attaura ba, ai, la’anannu ne.”

50 Nikodimu kuwa da ya je wurinsa dā, yana kuwa ɗaya daga cikinsu, ya ce musu,

51 “Ashe, shari’armu takan hukunta mutum tun ba a ji daga bakinsa ba, an kuma san abin da yake ciki?”

52 Suka amsa masa suka ce, “Kai ma Bagalile ne? Bincika mana ka gani, ai, ba wani annabi da zai bayyana a ƙasar Galili.”

Matar da aka Kama da Zina

[

53 Sai kowa ya tafi gida.