YOW 2

Fāra ta Zama Musu Alamar Ranar Ubangiji

1 Ku busa ƙaho, ku yi gangami,

A cikin Sihiyona, tsattsarkan

dutsen Allah!

Duk mutanen ƙasar za su yi rawar

jiki,

Domin ranar Ubangiji tana zuwa, ta

yi kusa.

2 Za ta zama rana ce mai duhu

dulum,

Ranar gizagizai ce baƙi ƙirin.

Runduna mai ƙarfi tana tasowa,

Kamar ketowar hasken safiya bisa

tsaunuka.

Faufau ba a taɓa ganin irinta ba,

Ba kuwa za a sāke ganin irinta ba.

3 Tana cinye shuke-shuke kamar wuta,

Ƙasa kamar gonar Adnin take kafin

ta zo,

Amma a bayanta ta zama hamada,

Ba abin da ya tsere mata.

4 Kamar doki take,

Tana gudu kamar dokin yaƙi.

5 Motsin tsallenta a kan duwatsu

kamar Motsin karusa ne.

Kamar kuma amon wutar da take cin

tattaka.

Kamar runduna mai ƙarfi wadda ta

ja dāgar yaƙi.

6 Da zuwanta mutane sukan firgita,

Dukan fuskoki sukan ɓaci.

7 Takan auka kamar mayaƙa,

Takan hau garu kamar sojoji,

Takan yi tafiya,

Kowa ta miƙe sosai inda ta sa

gaba,

Ba ta kaucewa.

8 Ba ta hawan hanyar juna,

Kowa tana bin hanyarta.

Takan kutsa cikin abokan gāba, ba a

iya tsai da ita.

9 Takan ruga cikin birni,

Takan hau garu a guje,

Takan hau gidaje,

Takan shiga ta tagogi kamar ɓarawo.

10 Duniya takan girgiza saboda ita,

Sammai sukan yi rawar jiki.

Rana da wata sukan duhunta,

Taurari kuwa sukan daina

haskakawa.

11 Ubangiji yakan umarci rundunarsa,

Rundunarsa mai cika umarninsa

babba ce, mai ƙarfi,

Gama ranar Ubangiji babba ce mai

banrazana.

Wa zai iya daurewa da ita?

Jinƙan Ubangiji

12 “Koyanzu,” in ji Ubangiji,

“Ku juyo wurina da zuciya ɗaya,

Da azumi, da kuka, da makoki,

13 Ku kyakkece zuciyarku, ba tufafinku

kaɗai ba.”

Ku komo wurin Ubangiji Allahnku.

Gama shi mai alheri ne, mai jinƙai,

Mai jinkirin fushi ne, mai yawan

ƙauna,

Yakan tsai da hukunci.

14 Wa ya sani ko Ubangiji Allahnmu zai

sāke nufinsa,

Ya sa mana albarka,

Har mu miƙa masa hadaya ta gari da

ta sha?

15 Ku busa ƙaho a Sihiyona,

Ku sa a yi azumi,

Ku kira muhimmin taro.

16 Ku tattara jama’a wuri ɗaya,

Ku tsarkake taron jama’a,

Ku tattara dattawa da yara,

Har da jarirai masu shan mama.

Ku sa ango ya fito daga cikin

turakarsa,

Amarya kuma ta fito daga cikin

ɗakinta.

17 Sai firistoci masu hidimar Ubangiji,

Su yi kuka a tsakanin shirayi da

bagade,

Su ce, “Ya Ubangiji, ka ceci

jama’arka,

Kada ka bar gādonka ya zama abin

zargi

Da abin ba’a a tsakiyar al’ummai.

Don kada al’ummai su ce,

‘Ina Allahnsu?’ ”

18 Sai Ubangiji ya ji kishin ƙasarsa,

Ya kuma ji ƙan mutanensa.

19 Sa’an nan ya ce musu,

“Ga shi, zan ba ku hatsi da ruwan

inabi, da mai,

Za ku ƙoshi.

Ba zan sa ku ƙara zama abin zargi ga

al’ummai ba.

20 Zan kawar muku da waɗanda suka

zo daga arewa,

Zan kori waɗansunsu zuwa cikin

hamada.

Zan kori sahunsu na gaba zuwa cikin

Tekun Gishiri,

Zan kori sahunsu na baya, zuwa

cikin Bahar Rum.

Gawawwakinsu za su yi ɗoyi.

Zan yi musu haka saboda dukan abin

da suka yi muku.”

21 Kada ki ji tsoro, ya ƙasa,

Ki yi farin ciki, ki yi murna,

Gama Ubangiji ne ya yi waɗannan

manyan al’amura.

22 Kada ku ji tsoro, ku dabbobin

saura,

Gama wuraren kiwo a jeji sun yi kore

shar.

Itatuwa suna ta yin ‘ya’ya,

Itacen ɓaure da kurangar inabi suna

ta yin ‘ya’ya sosai.

23 Ya ku mutanen Sihiyona, ku yi

murna,

Ku yi farin ciki da Ubangiji

Allahnku,

Gama ya ba ku ruwan farko

Domin shaidar gafarar da ya yi

muku,

Ya kwararo muku da ruwan farko da

na ƙarshe da yawa kamar dā.

24 Masussukai za su cika da hatsi,

Wuraren matse ruwan inabi za su

malala da ruwan inabi.

25 “Zan mayar muku da abin da kuka

yi hasararsa

A shekarun da fara ta cinye

amfaninku,

Wato ɗango da fara mai gaigayewa,

da mai cinyewa,

Su ne babbar rundunata wadda na

aiko muku.

26 Yanzu za ku ci abinci a wadace ku

ƙoshi,

Za ku yabi sunan Ubangiji

Allahnku,

Wanda ya yi muku abubuwa masu

banmamaki,

Ba kuma za a ƙara kunyatar da

mutanena ba.

27 Ku mutanen Isra’ila, za ku sani ina

cikinku,

Ni ne kuwa Ubangiji Allahnku, ba

wani kuma,

Ba kuma za a ƙara kunyatar da

mutanena ba.”

Za a Ba da Ruhun Allah

28 “Bayan wannan zan zubo Ruhuna a

kan jama’a duka,

‘Ya’yanku mata da maza za su iyar

da saƙona,

Tsofaffinku kuwa za su yi mafarkai,

Samarinku za su ga wahayi da yawa.

29 A lokacin zan zubo Ruhuna,

Har a kan barori mata da maza.

30 “Zan yi faɗakarwa a kan wannan

rana

A sararin sama da a duniya.

Za a ga jini, da wuta, da murtukewar

hayaƙi,

31 Rana za ta duhunta,

Wata zai zama ja wur kamar jini,

Kafin isowar babbar ranan nan mai

bantsoro ta Ubangiji.

32 Amma dukan waɗanda suka nemi

Ubangiji za su tsira.

Kamar yadda Ubangiji ya ce,

Akwai waɗanda suke a Dutsen

Sihiyona da Urushalima

Da za su tsira,

Waɗannan da Ubangiji ya zaɓa za su

tsira.”