YOW 1

Ɓarnar Fāra

1 Maganar Ubangiji zuwa ga Yowel, ɗan Fetuwel.

2 Ku dattawa, ku kasa kunne,

Bari kowa da kowa da yake cikin

Yahuza, ya kasa kunne.

Wani abu mai kamar wannan ya taɓa

faruwa a lokacinku,

Ko a lokacin kakanninku?

3 Ku faɗa wa ‘ya’yanku labarinsa,

‘Ya’yanku kuma su faɗa wa

‘ya’yansu,

‘Ya’yansu kuma su faɗa wa tsara

mai zuwa.

4 Abin da ɗango ya bari fara ta ci,

Abin da fara ta bari burduduwa ta

ci.

5 Ku farka, ku yi ta kuka, ku

bugaggu,

Ku yi kuka, ku mashayan ruwan

inabi,

An lalatar da ‘ya’yan inabin

Da ake yin sabon ruwan inabi da su.

6 Rundunar ta aukar wa ƙasarmu,

Tana da ƙarfi, ba ta kuma

ƙidayuwa,

Haƙoranta suna da kaifi kamar na

zaki.

7 Ta lalatar da kurangar inabinmu,

Ta cinye itatuwan ɓaurenmu.

Ta gaigaye ɓawo duka,

Saboda haka rassan sun zama fari

fat.

8 Ya jama’a, ku yi kuka

Kamar yarinyar da take makokin

rasuwar saurayinta.

9 Ba hatsi ko ruwan inabin

Da za a yi hadaya da su cikin

Haikalin.

Firistoci masu miƙa wa Ubangiji

hadaya suna makoki.

10 Ba kome a gonaki,

Ƙasa tana makoki,

Domin an lalatar da hatsin,

‘Ya’yan inabi sun bushe,

Itatuwan zaitun kuma sun yi yaushi.

11 Ya ku manoma, ku yi baƙin ciki,

Ku yi kuka, ku da kuke lura da

gonakin inabi,

Gama alkama, da sha’ir,

Da dukan amfanin gonaki sun

lalace.

12 Kurangar inabi ta bushe,

Itatuwan ɓaure kuma sun yi yaushi,

Rumman, da dabino, da gawasa,

Da dukan itatuwan gonaki sun

bushe.

Murna ta ƙare a wurin mutane.

13 Ya ku firistoci masu miƙa hadayu a

bagaden Ubangiji,

Ku sa tufafin makoki, ku yi kuka!

Ku shiga Haikali, ku kwana,

Kuna saye da tufafin makoki,

Gama ba hatsi ko ruwan inabi da za

a yi hadaya da su,

A cikin Haikalin Allahnku.

14 Ku sa a yi azumi,

Ku kira muhimmin taro.

Ku tara dattawa da dukan mutanen

ƙasar

A Haikalin Ubangiji Allahnku,

Ku yi kuka ga Ubangiji.

15 Taku ta ƙare a wannan rana!

Gama ranar Ubangiji ta kusa,

Halaka daga wurin Maɗaukaki ta zo.

16 An lalatar da amfanin gonaki a kan

idonmu,

Ba murna a Haikalin Allahnmu.

17 Itatuwa sun mutu a busasshiyar

ƙasa,

Ba hatsin da za a adana a rumbu,

Rumbuna sun lalace domin ba hatsi.

18 Dabbobi suna nishi!

Garkunan shanu sun ruɗe

Domin ba su da makiyaya.

Garkunan tumaki da awaki kuma

suna shan azaba.

19 Ina kuka a gare ka, ya Ubangiji,

Domin ciyayi da itatuwa sun bushe,

Sai ka ce wuta ce ta ƙone su.

20 Har ma namomin jeji suna kuka a

gare ka,

Domin rafuffuka sun bushe,

Ciyayi kuma sun bushe,

Sai ka ce wuta ce ta ƙone su.