ZAB 110

Ubangiji Ya Ba Sarkin da Ya Zaɓa Iko

1 Ubangiji ya ce wa Mai Girma, Sarkina,

“Zauna nan a damana,

Har in sa maƙiyanka a ƙarƙashin sawayenka.”

2 Tun daga Sihiyona Ubangiji zai faɗaɗa sarautarka, ya ce,

“Ka yi mulki bisa maƙiyanka.”

3 A ranar da za ka yi yaƙi da maƙiyanka,

Jama’arka za su kawo maka gudunmawa don kansu.

Kamar yadda raɓa take da sassafe,

Haka samarinka za su zo wurinka a tsarkakan tsaunuka.

4 Ubangiji ya yi muhimmin alkawari,

Ba kuwa zai fasa ba!

“Za ka zama firist har abada

Bisa ga tsabi’ar Malkisadik firist.”

5 Ubangiji yana damanka,

Zai kori sarakuna a ranar da ya husata.

6 Zai shara’anta wa dukan sauran al’umma,

Ya rufe fagen fama da gawawwaki,

Zai kori sarakunan duk duniya.

7 Sarkin zai sha ruwan rafin da yake kan hanya,

Ya wartsake ya sami ƙarfi.

Zai yi tsayawar nasara.