ZAB 141

Addu’ar Maraice ta Neman Keɓewa daga Mugunta

1 Ina kira gare ka, ya Ubangiji,

Ka taimake ni yanzu!

Ka saurare ni sa’ad da na kira gare ka.

2 Ka karɓi addu’ata kamar turaren ƙonawa,

Ka karɓi ɗaga hannuwa sama da na yi kamar hadayar maraice.

3 Ya Ubangiji, ka sa a yi tsaron bakina,

Ka sa mai tsaro a leɓunana.

4 Ka tsare ni daga son yin mugunta,

Ko kuma in haɗa kai da mugaye cikin muguntarsu,

Ka sa kada in taɓa yin tarayya da su a bukukuwansu!

5 Nagarin mutum ya iya hukunta ni, ya tsauta mini da alheri,

Zai zamar mini kamar an shafe kaina da mai,

Domin kullayaumi ina addu’a gāba da mugayen ayyuka.

6 Mutane za su yarda, cewa maganata gaskiya ce,

Sa’ad da aka jefo da masu mulkinsu ƙasa, daga ƙwanƙolin dutse,

7 Kamar itacen da aka faskare, aka daddatse,

Haka aka watsar da ƙasusuwansu a gefen kabari.

8 Amma ni, ya Ubangiji Allah, da nake dogara a gare ka,

Ina neman kiyayewarka,

Kada ka bar ni in halaka!

9 Ka kiyaye ni daga tarkunan da suka kafa mini,

Daga ashiftar masu aikata mugunta.

10 Ka sa mugaye su fāɗa cikin tarkunansu,

Ni kuwa in zo in wuce lafiya.