ZAB 52

Hukuncin Allah da Alherinsa

1 Me ya sa kake fariya da muguntarka,

Ya kai, babban mutum?

Ƙaunar Allah tana nan a koyaushe.

2 Kana shirya maƙarƙashiya don ka lalatar da waɗansu,

Harshenka kamar aska mai kaifi yake.

Kana ƙirƙiro ƙarairayi kullum.

3 Kana ƙaunar mugunta fiye da nagarta,

Kana kuwa ƙaunar faɗar ƙarya fiye da gaskiya.

4 Kana jin daɗin cutar mutane da maganganunka,

Ya kai, maƙaryaci!

5 Don haka Allah zai ɓata ka har abada,

Zai kama ka, yă jawo ka daga alfarwarka,

Zai kawar da kai daga ƙasar masu rai.

6 Adalai za su ga wannan, su ji tsoro,

Za su yi maka dariya, su ce,

7 “Duba, ga mutumin da bai dogara ga Allah

Don ya sami zaman lafiyarsa ba.

A maimakon haka, sai ya dogara ga wadatarsa.

Yana neman zaman lafiyarsa ta wurin muguntarsa.”

8 Amma ni, kamar itacen zaitun nake, wanda yake girma kusa da Haikalin Allah,

Ina dogara ga madawwamiyar ƙaunarsa har abada abadin.

9 Zan gode maka, ya Ubangiji,

Saboda abin da ka aikata.

Zan dogara gare ka,

Sa’ad da nake sujada tare da jama’arka,

Domin kai mai alheri ne.