ZAB 57

Addu’ar Neman Kuɓuta daga Tsanani

1 Ka yi mini jinƙai, ya Allah, ka yi jinƙai,

Gama na zo gare ka neman tsira.

Zan sami kāriya a ƙarƙashin fikafikanka,

Sai dukan hatsari ya wuce.

2 Zan yi kira ga Allah, Maɗaukaki,

Zan yi kira ga Allah, mai biyan dukan bukatata.

3 Daga sammai Allah zai amsa mini,

Zai kori waɗanda suka tasar mini,

Allah zai nuna mini madawwamiyar ƙaunarsa da amincinsa.

4 Raina yana tsakiyar zakoki,

Na kwanta a tsakiyar waɗanda suka yi niyyar cinye mutane.

Haƙoransu kamar māsu da kibau suke,

Harsunansu masu kaifi ne kamar takobi.

5 Ka bayyana girmanka ya Allah, a sararin sama,

Ɗaukakarka kuma a bisa dukan duniya!

6 Maƙiyana sun kafa tarko don su kama ni,

Damuwa ta fi ƙarfina.

Sun yi wushefe a kan hanyata,

Amma su da kansu suka fāɗa a ciki.

7 A shirye nake, ya Allah,

Na shirya sosai!

Zan raira waƙoƙi in yabe ka!

8 Ka farka, ya raina!

Ku farka, molona da garayata!

Zan sa rana ta farka!

9 Zan gode maka a cikin sauran al’umma, ya Ubangiji!

Zan yabe ka a cikin jama’a!

10 Madawwamiyar ƙaunarka ta kai har sammai,

Amincinka kuma har sararin sammai.

11 Ka bayyana girmanka, ya Allah, a sararin sama,

Ɗaukakarka kuma a bisa dukan duniya!