ZAB 1

Farin Ciki na Gaskiya

1 Albarka ta tabbata ga mutumin da

Ba ya karɓar shawarar mugaye,

Wanda ba ya bin al’amuran masu zunubi,

Ko ya haɗa kai da masu wasa da Allah.

2 Maimakon haka, yana jin daɗin karanta shari’ar Allah,

Yana ta nazarinta dare da rana.

3 Yana kama da itacen da yake a gefen ƙorama,

Yakan ba da ‘ya’ya a kan kari,

Ganyayensa ba sa yin yaushi,

Yakan yi nasara a dukan abin da yake yi.

4 Amma mugaye ba haka suke ba,

Su kamar yayi suke wanda iska take kwashewa.

5 Allah kuwa zai hukunta mugaye,

Masu zunubi kuwa za a ware su daga adalai.

6 Gama Ubangiji yana lura da al’amuran adalai,

Amma al’amuran mugaye za su watse.