AMOS 4

1 Ku kasa kunne ga wannan, ya ku

matan Samariya,

Ku da kuka yi ƙiba kamar

turkakkun shanu,

Ku da kuke wulakanta kasassu,

Kuna yi wa matalauta danniya,

Kukan umarci mazajenku,

Ku ce, “Kawo mini abin sha!”

2 Da yake Ubangiji Mai Tsarki ne

Ya riga ya yi alkawari,

Ya ce, “Hakika kwanaki za su zo

Da za a jawo ku da ƙugiyoyi,

Kowannenku zai zama kamar kifi a

ƙugiya.

3 Za a kwashe ku, a fitar da ku

Ta inda garu ya tsage na mafi kusa

duka, a jefar.”

Isra’ila Sun Kāsa Koyo

4 Ubangiji ya ce,

“Jama’ar Isra’ila,

Ku tafi Betel, tsattsarkan wuri,

Ku yi ta zunubi!

Ku tafi Gilgal ku ƙara zunubi!

Ku yi ta kawo dabbobi sadaka

kowace safiya.

A kowace rana ta uku

Ku yi ta ba da zaka.

5 Ku miƙa abincinku hadaya ta

godiya.

Ku yi ta yin fariya da hadayarku ta

yardar rai!

Gama irin abin da kuke jin daɗin yi

ke nan.”

6 Ubangiji ya ce,

“Ai, ni ne, na sa a yi yunwa a

biranenku.

Shi ya sa ba ku da abinci.

Duk da haka ba ku juyo gare ni ba.

7 Na hana wa shuke-shukenku ruwa

A lokacin da suka fi bukata.

Na sa a yi ruwa a wani birni,

A wani birni kuwa na hana,

Wata gonar ta sami ruwan sama,

Amma wadda ba ta samu ba ta

bushe.

8 Ƙishirwa ta sa jama’a su tafke har

birane biyu ko uku

Suka tafi neman ruwa a birnin da

suke maƙwabtaka da shi,

A nan ma ba su sami isasshen ruwan

sha ba,

Duk da haka ba ku komo wurina

ba.

9 “Na sa darɓa, da domana

Su lalatar da amfanin gonakinku.

Fāra kuma ta cinye lambunanku

Da gonakin inabinku, da itatuwan

ɓaurenku,

Da na zaitun ɗinku.

Duk da haka ba ku komo wurina ba.

10 “Na aukar muku da annoba irin

wadda na aukar wa Masar.

Na karkashe samarinku a wurin

yaƙi,

Na kwashe dawakanku.

Na cika hancinku da ɗoyin

sansaninku.

Duk da haka ba ku komo wurina ba.

11 “Na hallakar da waɗansunku

Kamar yadda na hallakar da Saduma

da Gwamrata.

Kamar sanda kuke, wanda aka fizge

daga wuta.

Duk da haka ba ku komo wurina

ba.

12 Saboda haka, jama’ar Isra’ila,

Ga abin da zan yi muku,

Zan kuwa yi shi duk,

Sai ku yi shirin zuwa gaban

Ubangiji.”

13 Allah ne ya yi duwatsu

Ya kuma halicci iska.

Ya sanar da nufinsa ga mutum,

Ya juya rana ta zama dare.

Yana sarautar duniya duka.

Sunansa kuwa Ubangiji Maɗaukaki!