AMOS 6

Halakar Isra’ila

1 Taku ta ƙare, ku da kuke zaman

sakewa a Sihiyona,

Da ku da kuke tsammani kuna

zaman lafiya a Samariya,

Ku da kuke manyan mutane

Na wannan babbar al’umma ta

Isra’ila,

Waɗanda jama’a suke zuwa a gare su

neman taimako!

2 Ku je ku duba a birnin Kalne.

Sa’an nan ku zarce zuwa babban

birnin Hamat,

Har zuwa birnin Gat ta Filistiyawa.

Sun fi mulkin Yahuza da Isra’ila ne?

Ko kuwa, yankin ƙasarsu ya fi

naku?

3 Kuna ƙoƙari ku kauce wa wannan

rana ta masifa,

Amma ga shi, goyon bayan hargitsi

kuke ta yi,

Ta wurin ayyukanku.

4 Taku ta ƙare, ku da kuke kwance

kan gadajen hauren giwa,

Kuna jin daɗin miƙe jiki a dogayen

kujerunku,

Ku ci naman maraƙi da na rago.

5 Kukan so ku tsara waƙoƙi kamar

yadda Dawuda ya yi,

Ku raira su da garayu.

6 Da manyan kwanoni kuke shan

ruwan inabi,

Ku shafe jiki da mai mafi kyau,

Amma ba ku yin makoki saboda

lalacewar Isra’ila.

7 Don haka, ku ne na fari da za a sa su

yi ƙaura

Bukukuwanku da shagulgulanku za

su ƙare.

8 Ubangiji kansa ne ya rantse.

Ubangiji Allah Mai Runduna ya ce,

“Ba na son girmankai na jama’ar

Isra’ila.

Ba na son fādodinsu.

Zan ba da birnin da dukan abin da

yake cikinsa ga abokan gābansu.”

9 Ko da a ce mutum goma ne suka ragu a gida guda, duk za su mutu.

10 Sa’ad da dangin mamacin ya shiga don ya fitar da gawar, ya ƙone, sai ya yi kira ga ko wane ne da yake ɓoye a gidan, ya ce, “Ko akwai wani kuma a nan?”

Sai a amsa, “A’a.”

Zai ce, “Kul! Kada a ambaci sunan Ubangiji.”

11 Sa’ad da Ubangiji ya ba da umarni, babban gida da ƙarami rushewa za su yi.

12 Dawakai sukan yi sukuwa a

duwatsu?

Ana huɗan teku da garmar

shanu?

Duk da haka kuka mai da adalci

dafi,

Kuka mai da nagarta, mugunta.

13 Kuna fariyar cin garin Lodebar, wato

wofi, da yaƙi.

Kun ce, “Ƙarfinmu ya isa har mu ci

Karnayim, wato ƙaho biyu, da

yaƙi.”

14 Ubangiji Allah Mai Runduna

kansa, ya amsa ya ce,

“Zan aiko da wata al’umma ta yi

gāba da ku, ya Isra’ilawa.

Za ta matse muku

Tun daga mashigin Hamat wajen

arewa,

Har zuwa Kwarin Urdun a kudu.”