IRM 30

Tabbatarwar Komowa daga Zaman Talala

1 Ubangiji ya yi magana da Irmiya, ya ce,

2 “Ni Ubangiji Allah na Isra’ila na ce, ‘Ka rubuta dukan maganar da na faɗa maka a littafi.

3 Gama kwanaki suna zuwa sa’ad da zan komo da mutanena, wato Isra’ila da Yahuza. Zan komo da su zuwa ƙasar da na ba kakanninsu, za su kuwa mallake ta,’ ni Ubangiji na faɗa.”

4 Waɗannan ne maganar da Ubangiji ya faɗa a kan Isra’ila da Yahuza.

5 “Ni Ubangiji na ce,

Mun ji kukan gigitacce,

Kukan firgita ba kuma salama.

6 Yanzu ku tambaya, ku ji,

Namiji ya taɓa haihuwa?

To, me ya sa nake ganin kowane

namiji yana riƙe da kwankwaso,

Kamar mace mai naƙuda,

Fuskar kowa kuma ta yi yaushi?

7 Kaito, gama wannan babbar rana ce,

Ba kuma kamarta,

Lokaci ne na wahala ga Yakubu,

Duk da haka za a cece shi daga

cikinta.”

8 Ubangiji Mai Runduna ya ce, “A wannan rana zan karya karkiya da take a wuyansu, in cire musu ƙangi, ba kuma za su ƙara zama bayin baƙi ba.

9 Amma za su bauta mini, ni Ubangiji Allahnsu, da Dawuda sarkinsu, wanda zan tayar musu da shi.”

10 Ubangiji ya ce,

“Kada ka ji tsoro, ya barana

Yakubu,

Kada kuma ka yi fargaba, ya

Isra’ila,

Gama zan cece ka daga ƙasa mai

nisa,

Zan kuma ceci zuriyarka daga ƙasar

bautarsu.

Yakubu zai komo, ya yi zamansa rai

a kwance,

Ba kuwa za a tsoratar da shi ba.

11 Gama ina tare da kai don in cece ka,

Zan hallaka dukan al’ummai sarai,

Inda na warwatsa ku.

Amma ku ba zan hallaka ku ba,

Zan hore ku da adalci,

Ba yadda za a yi in ƙyale ku ba

hukunci,

Ni Ubangiji na faɗa.”

12 Ubangiji ya ce,

“Rauninku ba ya warkuwa,

Mikinku kuwa mai tsanani ne

ƙwarai.

13 Ba wanda zai kula da maganarku,

Ba magani domin mikinku,

Ba za ku warke ba.

14 Dukan masu ƙaunarku sun manta

da ku,

Ba su ƙara kulawa da ku,

Domin na yi muku bugu irin na

maƙiyi.

Na yi muku horo irin na maƙiyi

marar tausayi,

Domin laifofinku masu girma ne,

Domin zunubanku da yawa suke.

15 Don me kuke kuka a kan

rauninku?

Ciwonku ba zai warke ba.

Saboda laifofinku masu girma ne,

Domin zunubanku da yawa suke,

Shi ya sa na yi muku waɗannan

abubuwa.

16 Domin haka dukan waɗanda suka

cinye ku, za a cinye su,

Dukan maƙiyanku, kowane ɗayansu

zai tafi bauta,

Waɗanda suka washe ku, za a washe

su.

Dukan waɗanda suka kwashe ku

ganima, su ma za a kwashe su

ganima.

17 Zan mayar muku da lafiyarku,

Zan kuma warkar da raunukanku,

Ko da yake maƙiyanku suna

kiranku yasassu,

Suna cewa, ‘Ai, Sihiyona ce, ba

wanda ya kula da ita.’

Ni Ubangiji na faɗa.”

18 Ubangiji ya ce,

“Ga shi, zan komar wa alfarwar

Yakubu arzikinta,

Zan kuma nuna wa wuraren zamansa

jinƙai,

Za a sāke gina birnin a kufansa,

Fādar kuma za ta kasance a inda

take a dā.

19 Daga cikinsu za a ji waƙoƙin godiya.

Da muryoyin masu murna.

Zai riɓaɓɓanya su, ba za su zama

kaɗan ba,

Zan kuwa ɗaukaka su, ba za a

ƙasƙantar da su ba.

20 ‘Ya’yansu za su zama kamar dā,

Jama’arsu kuma za su kahu a

gabana,

Zan hukunta dukan waɗanda suka

zalunce su.

21 Sarkinsu zai zama ɗaya daga

cikinsu,

Mai mulkinsu kuma zai fito daga

cikinsu.

Zan kawo shi kusa, zai kuwa kusace

ni,

Gama wane ne zai yi ƙarfin hali ya

kusace ni? Ni Ubangiji na faɗa.

22 Za ku zama mutanena,

Ni kuwa zan zama Allahnku.”

23 Ga hadirin hasalar Ubangiji ya taso,

wato iskar guguwa,

Zai huce a kan mugaye.

24 Zafin fushin Ubangiji ba zai huce ba,

Sai ya aikata, ya kammala abubuwan

da ya yi niyya a tunaninsa.

A nan gaba mutanensa za su fahimci

wannan.