IRM 31

1 Ubangiji ya ce, “Lokaci yana zuwa da zan zama Allah na dukan iyalan Isra’ila, za su kuwa zama jama’ata.”

2 Haka Ubangiji ya ce, “Jama’ar da

suka tsere wa takobi,

Sun sami alheri a cikin jeji,

A sa’ad da Isra’ila suka nemi

hutawa.”

3-4 Ubangiji ya bayyana gare ni tun

daga nesa cewa,

“Ya Isra’ila, budurwa!

Na kusace ki da madawwamiyar

ƙaunata,

Ba zan fasa amintacciyar ƙaunata a

gare ki ba.

Zan sāke gina ki,

Za ki kuwa ginu,

Za ki ɗauki kayan kaɗe-kaɗe,

Za ki shiga rawar masu murna.

5 Za ki sāke dasa gonar inabi

A kan duwatsun Samariya,

Masu dashe za su dasa,

Za su mori ‘ya’yan.

6 Gama rana tana zuwa sa’ad da mai

tsaro zai yi kira

A ƙasar tudu ta Ifraimu, ya ce,

‘Ku tashi mu haura zuwa Sihiyona

Zuwa wurin Ubangiji Allahnmu.’ ”

7 Ga abin da Ubangiji ya ce,

“Raira wa Yakubu waƙar farin ciki

da ƙarfi,

Ku ta da murya saboda shugaban

al’ummai,

Ku yi shela, ku yi yabo, ku ce,

‘Ya Ubangiji ka ceci jama’arka,

Wato ringin mutanen Isra’ila,’

8 Ga shi, zan fito da su daga ƙasar

arewa,

Zan tattaro su daga manisantan

wurare na duniya,

Tare da su makafi da guragu,

Da mace mai goyo da mai naƙuda,

Za su komo nan a babbar ƙungiya.

9 Da kuka za su komo.

Da ta’aziyya zan bishe su, in komar

da su,

Zan sa su yi tafiya a gefen rafuffukan

ruwa,

A kan miƙaƙƙiyar hanya, inda ba

za su yi tuntuɓe ba.

Gama ni uba ne ga Isra’ila,

Ifraimu kuwa ɗan farina ne.”

10 “Ku ji maganar Ubangiji,

Ya ku al’ummai,

Ku yi shelarsa har a ƙasashen da suke

nesa, na gāɓar teku.

Ku ce, ‘Shi wanda ya warwatsa

Isra’ila zai tattaro ta,

Zai kiyaye ta kamar yadda makiyayi

yakan kiyaye garkensa.’

11 Gama Ubangiji ya fanshi Yakubu.

Ya fanshe shi daga hannuwan

waɗanda suka fi ƙarfinsa.

12 Za su zo su raira waƙa da ƙarfi,

A bisa ƙwanƙolin Sihiyona,

Za su yi annuri saboda alherin

Ubangiji,

Saboda hatsi, da ruwan inabi, da

mai,

Saboda ‘ya’yan tumaki da na shanu.

Rayuwarsu za ta zama kamar

lambu,

Ba za su ƙara yin yaushi ba.

13 Sa’an nan ‘yan mata za su yi rawa

da farin ciki,

Samari da tsofaffi za su yi murna.

Zan mai da makokinsu ya zama

murna,

Zan ta’azantar da su, in ba su farin

ciki maimakon baƙin ciki.

14 Zan yi wa ran firistoci biki da

wadata,

Jama’ata za su ƙoshi da alherina,

Ni Ubangiji na faɗa.”

15 Ga abin da Ubangiji ya ce,

“An ji murya daga Rama,

Muryar baƙin ciki da kuka mai zafi,

Rahila tana kuka saboda ‘ya’yanta,

ba su.

16 Ki yi shiru, ki daina kuka,

Ki shafe hawaye daga idanunki.

Za a sāka miki wahalarki,

Za su komo daga ƙasar abokin gāba,

Ni Ubangiji na faɗa.

17 Akwai sa zuciya dominki a nan

gaba,

Ni Ubangiji na faɗa.

‘Ya’yanki za su komo ƙasarsu.

18 “Na ji Ifraimu yana baƙin ciki, yana

cewa,

‘Ka hore ni, na kuwa horu,

Kamar ɗan maraƙin da ba shi da

horo,

Ka komo da ni don in zama kamar

yadda nake a dā,

Gama kai ne Ubangiji Allahna.

19 Gama na tuba saboda na rabu da

kai,

Bayan da aka ganar da ni, sai na

sunkuyar da kai,

Kunya ta kama ni, na gigice,

Domin ina ɗauke da wulakancin

ƙuruciyata.’

20 Ashe, Ifraimu ba ƙaunataccen

ɗana ba ne?

Ashe, shi ba ɗan gaban goshina ba

ne?

A duk lokacin da na ambace shi a

kan muguntarsa

Nakan tuna da shi da ƙauna.

Saboda na ƙwallafa zuciyata a

kansa,

Hakika zan yi masa jinƙai, ni

Ubangiji na faɗa.”

21 Ki kafa wa kanki alamun hanya,

Ki kafa wa kanki shaidu,

Ki lura da gwadabe da kyau,

Hanyar da kin bi, kin tafi.

Ya budurwa Isra’ila, ki komo,

Komo zuwa biranen nan naki.

22 Har yaushe za ki yi ta shakka,

Ya ke ‘yar marar bangaskiya?

Gama Ubangiji ya halitta sabon abu

a duniya,

Mace ce za ta kāre namiji.”

23 Haka Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra’ila, ya ce, “Nan gaba za su sāke yin magana a ƙasar Yahuza da biranenta a sa’ad da na mayar musu da dukiyarsu.

‘Ubangiji ya sa maka albarka,

Ya wurin zaman adalci,

Ya tsattsarkan tudu!’

24 Yahuza kuwa da dukan biranenta za su zauna tare a can, da manoma, da makiyaya, da garkunansu.

25 Gama zan biya bukatar waɗanda suka gaji, in wartsakar da waɗanda ransu ya yi yaushi.”

26 Irmiya ya farka, ya ce, “Ina kuwa cikin barcina mai daɗi sai na farka na duba.”

Sabon Alkawari

27 “Ni Ubangiji na ce, ga shi, zan sa mutane da dabbobi su cika ƙasashen Isra’ila da na Yahuza.

28 Zai zama kamar yadda na lura da su don a tumɓuke su, a rushe su, a lalatar da su, a kawo musu masifa, haka kuma zan lura da su, a kuma dasa su, ni Ubangiji na faɗa.

29 A waɗannan kwanaki ba za su ƙara cewa,

‘Ubanni suka ci ‘ya’yan inabi masu

tsami,

Haƙoran ‘ya’ya suka mutu’ ba.

30 Amma kowa zai mutu saboda

zunubin kansa,

Wanda ya ci inabi masu tsami,

Shi ne haƙoransa za su mutu.”

31 Ubangiji ya ce, “Ga shi, kwanaki suna zuwa da zan yi sabon alkawari da mutanen Isra’ila da na Yahuza.

32 Ba irin wanda na yi da kakanninsu ba, sa’ad da na fito da su daga ƙasar Masar, alkawarin da suka karya, ko da yake ni Ubangijinsu ne, ni Ubangiji na faɗa.

33 Amma wannan shi ne alkawarin da zan yi da mutanen Isra’ila bayan waɗancan kwanaki, ni Ubangiji na faɗa. Zan sa dokokina a cikinsu, zan rubuta su a zukatansu, zan zama Allahnsu, su kuma za su zama jama’ata.

34 Mutum ba zai ƙara koya wa maƙwabcinsa, ko ɗan’uwansa cewa, ‘Ka san Ubangiji’ ba, gama su duka za su san ni, tun daga ƙarami har zuwa babba. Zan gafarta musu laifofinsu, ba kuwa zan ƙara tunawa da zunubansu ba.”

35 Haka Ubangiji ya ce,

Shi wanda ya ba da rana ta haskaka

yini,

Ya sa wata da taurari su ba da haske

da dare,

Shi ne yakan dama teku, ya sa

raƙumanta su yi ruri,

Sunansa Ubangiji Mai Runduna.

36 “Idan dai wannan kafaffiyar ka’ida

ta daina aiki a gabana,

Ni Ubangiji na faɗa,

To, ashe, zuriyar Isra’ila za ta daina

zama al’umma a gabana ke nan

har abada.

37 Idan a iya auna sammai a kuma iya

bincike tushen duniya a ƙarƙas,

To, ashe, zan watsar da dukan

zuriyar Isra’ila ke nan saboda

dukan abin da suka yi,

Ni Ubangiji na faɗa.

38 “Ga shi, kwanaki suna zuwa da za a sāke gina birnin domin Ubangiji, ni Ubangiji na faɗa, tun daga hasumiyar Hananel zuwa yamma, har zuwa Ƙofar Kan Kusurwa.

39 Sa’an nan ma’aunin zai daɗa gaba, har ya kai tudun Gareb, sa’an nan ya nausa zuwa Gowa.

40 Dukan filin kwarin gawawwaki da toka, da dukan filaye har zuwa rafin Kidron zuwa kan kusurwar Ƙofar Doki wajen gabas, za su zama mai tsarki ga Ubangiji. Ba za a ƙara tumɓuke shi ko a rushe shi ba har abada.”