ROM 16

Gaisuwa

1 Ga ‘yar’uwarmu Fibi ina sada ku da ita, ita ma kuwa mai hidimar ikilisiya ce a Kankiriya.

2 Ku karɓe ta da hannu biyu biyu saboda Ubangiji, ta halin da ya dace da tsarkaka. Ku kuma taimake ta da duk irin abin da ta nemi taimako a gare ku, domin ita ma tā taimaki mutane da yawa, har ma da ni kaina.

3 Ku gai da Bilkisu da Akila, abokan aikina a cikin Almasihu Yesu,

4 waɗanda suka kasai da ransu saboda ni, ba kuwa ni kaɗai nake gode musu ba, har ma da dukkan ikilisiyoyin al’ummai.

5 Ku kuma gai da ikilisiyar da take taruwa a gidansu. Ku gai da ƙaunataccena Abainitas, wanda yake shi ne ya fara bin Almasihu a ƙasar Asiya.

6 Ku gai da Maryamu, wadda ta yi muku aiki ƙwarai da gaske.

7 Ku gai da Andaranikas da Yuniyas, ‘yan’uwana, abokan ɗaurina, waɗanda suke shahararru a cikin manzanni, har ma sun riga ni bin Almasihu.

8 Ku gai da Amfiliyas, ƙaunataccena a cikin Ubangiji.

9 Ku gai da Urbanas abokin aikinmu a cikin Almasihu, da kuma ƙaunataccena Istakis.

10 Ku kuma gai da Abalis, amintaccen nan a cikin Almasihu. Ku gai da jama’ar Aristobulus.

11 Ku gai da ‘dan’uwana Hirudiyan. Ku gai da waɗanda suke na Ubangiji a cikin jama’ar Narkisas.

12 Ku gai da Tarafina da Tarafusa, masu aikin Ubangiji. Ku gai da Barsisa, ƙaunatacciya, wadda ta yi aikin Ubangiji ƙwarai da gaske.

13 Ku gai da Rufas, fitaccen mai bin Ubangiji, da kuma mahaifiyarsa, tawa kuma.

14 Ku gai da Asinkiritas, da Filiguna, da Hamisa, da Baturobas, da Hamasa, da kuma ‘yan’uwan da suke tare da su.

15 Ku gai da Filulugusa, da Yuliya, da Niriyas, da ‘yar’uwarsa, da Ulumfas da kuma dukan tsarkakan da suke tare da su.

16 Ku gaggai da juna da tsattsarkar sumba. Dukan ikilisiyoyin Almasihu suna gaishe ku.

17 Ina roƙonku, ‘yan’uwa, ku yi hankali fa da masu raba tsakani, saɓanin koyarwar da kuka koya, suna sa tuntuɓe. Ku yi nesa da su.

18 Ai, irin waɗannan mutane ba sa bauta wa Ubangijinmu Almasihu, sai dai cikinsu. Ta romon kunne da daɗin baki suke yaudarar masu sauƙin kai.

19 Amma ku kam, ai, kowa ya san biyayyarku, shi ya sa nake farin ciki da ku. Sai dai ina so ku gwanance da abin da yake nagari, amma ya zama ba ruwanku da mugunta.

20 Allah mai ba da salama kuwa, zai sa ku tattake Shaiɗan da hanzari. Alherin Ubangijinmu Yesu Almasihu yă tabbata a gare ku.

21 Timoti, abokin aikina, yana gaishe ku, haka kuma Lukiyas da Yason da kuma Susibataras, ‘yan’uwana.

22 Ni Tartiyas, mai rubuta wasiƙar nan, ina gaishe ku saboda Ubangiji.

23 Gayus, mai masaukina, mai kuma saukar da dukan ‘yan ikilisiya, yana gaishe ku. Arastas, ma’ajin gari, da kuma ɗan’uwanmu Kawartas, suna gaishe ku.

24 Alherin Ubangijinmu Yesu Almasihu yă tabbata a gare ku duka. Amin, Amin.

Ƙarasawa da Yabo

25 Ɗaukaka tă tabbata ga mai ikon ƙarfafa ku bisa ga bisharata, bisa ga wa’azin Yesu Almasihu, wadda ta gare ta ne aka bayyana asirin nan da yake ɓoye tun fil’azal.

26 Asirin nan kuwa sanar da shi ga dukan al’ummai, ta wurin littattafan annabawa, bisa ga umarnin Allah Madawwami, domin a jawo su, su gaskata, su yi biyayya.

27 Ɗaukaka tă tabbata har abada ga Allah Makaɗaicin hikima ta wurin Yesu Almasihu! Amin, Amin.