ZAB 123

Addu’ar Neman Jinƙai

1 Ya Ubangiji, ina zuba ido gare ka,

A Sama inda kake mulki.

2 Kamar yadda bara yake dogara ga maigidansa,

Baranya kuma ga uwargijiyarta,

Haka nan muke zuba ido gare ka, ya Ubangiji Allahnmu,

Har mu sami jinƙanka.

3 Ka yi mana jinƙai, ya Ubangiji, ka yi mana jinƙai,

An gwada mana wulakanci matuƙa!

4 Attajirai sun daɗe suna ta yi mana ba’a,

Azzalumai masu girmankai sun raina mu!