ZAB 136

Waƙar Godiyar Ƙaunar Allah

1 Ku gode wa Ubangiji domin shi mai alheri ne,

Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.

2 Ku gode wa Allahn da ya fi dukan alloli girma,

Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.

3 Ku gode wa Ubangijin dukan iyayengiji,

Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.

4 Shi kaɗai ne yake aikata mu’ujizai masu girma,

Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.

5 Ta wurin hikimarsa ya halicci sammai,

Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.

6 Ya kafa duniya a bisa kan ruwa mai zurfi,

Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.

7 Shi ne ya halicci rana da wata,

Gama ƙaunarsa madawwamiya ce,

8 Rana don ta yi mulkin yini,

Gama ƙaunarsa madawwamiya ce,

9 Wata da taurari kuwa don su yi mulkin dare,

Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.

10 Shi ya karkashe ‘ya’yan fari maza, na Masarawa,

Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.

11 Shi ya fito da jama’ar Isra’ila daga cikin Masar,

Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.

12 Da ƙarfinsa da ikonsa ya fito da su,

Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.

13 Shi ne ya keta Bahar Maliya biyu,

Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.

14 Shi ya bi da jama’arsa ta cikin tekun,

Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.

15 Shi ne ya sa ruwa ya ci Fir’auna da rundunarsa,

Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.

16 Ya bi da jama’arsa cikin hamada,

Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.

17 Ya karkashe sarakuna masu iko,

Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.

18 Ya karkashe shahararrun sarakuna,

Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.

19 Ya kashe Sihon, Sarkin Amoriyawa,

Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.

20 Ya kashe Og, Sarkin Bashan,

Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.

21 Ya ba da ƙasarsu ga jama’arsa,

Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.

22 Ya ba da ita ga bawansa Isra’ila,

Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.

23 Bai manta da mu sa’ad da aka yi nasara da mu ba,

Gama ƙaunarsa madawwamiyar ce.

24 Ya ‘yantar da mu daga abokan gābanmu,

Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.

25 Yana ba da abinci ga dukan mutane da dabbobi,

Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.

26 Ku yi wa Allah sa Sama godiya,

Gama ƙaunarsa madawwamiyar ce.