ZAB 138

Godiya domin Alherin Ubangiji

1 Da zuciya ɗaya nake gode maka, ya Ubangiji,

Ina raira waƙar yabonka a gaban alloli.

2 Na durƙusa a gaban tsattsarkan Haikalinka

Ina yabon sunanka.

Sabili da madawwamiyar ƙaunarka da amincinka,

Saboda ka nuna ɗaukakarka da umarnanka.

3 Ka amsa mini sa’ad da na yi kira gare ka,

Da ƙarfinka ka ƙarfafa ni.

4 Dukan sarakunan duniyar nan za su yabe ka, ya Ubangiji,

Gama sun riga sun ji alkawaranka.

5 Za su raira waƙa a kan abin da Ubangiji ya yi,

Za su raira waƙa kuma a kan ɗaukakarsa mai girma.

6 Ko da yake Ubangiji yana can Sama,

Duk da haka yana kulawa da masu kaɗaici.

Masu girmankai kuwa ba za su iya ɓoye kansu daga gare shi ba.

7 Ko lokacin da nake tsakiyar wahala,

Za ka kiyaye ni lafiya,

Ka yi gāba da abokan gābana, waɗanda suka husata,

Za ka kuwa cece ni da ikonka.

8 Za ka aikata kowane abu da ka alkawarta mini,

Ya Ubangiji, ƙaunarka madawwamiya ce har abada.

Ka cikasa aikin da ka fara.