ZAB 75

Allah Ya Ƙasƙantar da Mugaye, Ya Ɗaukaka Adalai

1 Muna yabonka, ya Allah, muna yabonka!

Muna shelar sunanka mai girma,

Muna kuwa faɗa abubuwan banmamaki da ka aikata!

2 “Na ƙayyade lokacin yin shari’a,” in ji Ubangiji Allah,

“Zan kuwa yi shari’ar gaskiya.

3 Ko da duniya da dukan waɗanda yake zaune cikinta za su ɓace,

Zan ƙarfafa harsashin gininta.

4 Na faɗa wa masu girmankai kada su yi taƙama,

Na kuma faɗa wa mugaye kada su yi fāriya,

5 Na dai faɗa musu su daina yanga,

Su daina yin taƙama.”

6 Hukunci ba daga gabas, ko yamma,

Ko daga kudu, ko arewa yake zuwa ba.

7 Allah yake yin shari’a,

Yana ƙasƙantar da waɗansu, ya kuma ɗaukaka waɗansu.

8 Ubangiji yana riƙe da ƙoƙo,

Cike da sabon ruwan inabi mai ƙarfi,

Yana zuba shi, dukan mugaye kuwa suna ta sha,

Suka shanye shi ƙaƙaf.

9 Amma har abada ba zan daina yin magana a kan Allah na Yakubu ba,

Ko in daina raira yabbai gare shi.

10 Shi zai karya ikon mugaye,

Amma za a ƙara wa masu adalci ƙarfi.